Wednesday 27 April 2016

Halaccin Sarauta Episode 5

The continuation of Halaccin Sarita

ruwa ta debo ta watsa mishi,tuni yafarka sannan tace "wuce muje" har toilet takaishi tazuba mar ruwan zafi sannan tarufo tafito, bayan minti goma saigashi yafito yana bin bango sanye da jallabiyan mata, abun yaso yabata dariya saikawai yafada kan gadon, wani matsanancin bacci ne ya kwasheshi yadda taga rana haka taga dare tsoronta karya farka yamata wani abu, saida asuba bacci barawo yakwasheta, karfe goma daidai yafarka ga mamakinsa yaganshi akan gado lullube da bargo, tunanin meya faru yafarayi, yatuna wani abun yamanta wani anma yamike ganin jallabiya ajikinshi ya tsorata kodai yazo daki da karuwa ne baisaniba?" Bashiri yafara neman kayansa anma baiganiba nan yahango aliya akan kujera saidai baiga fuskarba saboda gashinta yazubo tagaban fuskan, yaje ahankali yabude bakace sedai bakinta mai kyau ne, yabayyana kalan fatarta da kyan fuskanta, yakare mata kallo gabanshi na tsananta faduwa numfashinsa ne yahade danata hakan yasa ta farka dasauri ganinshi akanta yasa tace "meye haka? " yadan bata rai sannan yace " kinsan da yarima kike magana ko, akanme zaki kawoni nan, ko nina kawo kaina ? Bani kayana nasaka, takalleshi ta tabbata yadawo hayyacinsa sannan tamike tsakar gyda tanufa ta tattaro masa tareda cewa "kayi amai ajikinsu na wankema, sannan nan gaba in zakace shaye shayenka ka tattari dogaranka,my plan is not saving some kind of soul" abun ya harzukashi anma yashare toilet yashiga yasaka kayan sannan yafito baiko cemata uffan ba balle nagode yafice, taja tsaki tareda cewa "halinsa sak uwarsa" nan ta harhada abunda zata hada sannan tamaida kayan bayinta tarufo gidan saboda tassn yagane gidan karyace zaimata wani mugunta. Fada takoma inda ta tsinci bilki cikin tashin hankali tana cewa ina kikaje? Aliya tace "gaysuwa" bilki taja tsuka tareda cewa "yanzu da umma uwar soro tazo ta yi kirge fa?" Ganin bilki zata dameta yasa aliya tafice tabarta, fannin falmata ta isa bayan anmata iso tagayamata tadawo, dawowanta daki taji bilki nafada itada wata baiwa agefe. Ai yarima bai kwana agyda ba, jiya anata nemenshi harta wayoyinsa yaki dauka,ko yakoma shan giyansa da neman mata, sunata surutai anan aliya tatuna ashefa yaga fuskanta, donhaka dole tayu kaffa kaffa da shi acikin gidan, hakan kuwa tayi suka koma yin wasan boye boye duk inda taganshi canja hanya take Watarana dasafe abisa aladan gidan matan sarkin zasu hadu suje gaida sarki dasu da yaransu insun dawo kuma, sai suma maaikatan sumika nasu gaysuwan gun matan sarki, ahanyan dawowa falmata tace anemo mata yarima yusuf, shiganta bayan wasu mintinai saigashi yashigo yazauna akan kujerar dake kallon nata, "inaso ka kasa kunne kasaurareni" tafada cikin rashin faraa, "shaye shayenka yafara yawa, jiya abuge aka kawoka. So kake kasakani a magana? Wazaiba wa dan giya sarki? Yakamata ka nutsu wlh tun kafin lokaci yakurema," baice komi ba yana kallon hanyan kofa wanda jakadiya ta aiki aliya tashigo da tray, ganinta dayayi yatuna ta cak, itama tana ganinshi saidata tsorata anma tayi kaman ba ita bane ya ce "KE! Zonan," ta iso kanta akasa "dago fuskanki" tadago yatabbatar itane anma yagane mahaifiyarsa donhaka yace "jeki" falmata tace "meyene?" "Tamin kama da watane" alokacin aliya ta ajiye tray din tajuya tafice, saida falmata ta tugeshi baice uffan ba yafice, jakadiya tabada shawaran amasa aure dawuri ko mace zata nutsarshi, namiji mai gagara ai macece mai nutsar dashi, anma falmata tace itakam sam bazaa kawo wacce zata kwace mata danta ba, anma tana ganin karshe abunda zatayi kenan, acan fannin kuwa yanashiga falonsa, yakira bilki wacce itace take masa hidimansa. Yabukaci yasan sunan baiwar datake fannin uwarsa, anan bilki ta tsorata sosai duk da tagane bayaninsa anma tayi kaman bataganeba, daya watsa mata wani tsawa bashiri tace masa aliya sunanta. Kuma tataba bauta agunsa yace acanjata, anan yashiga tunani yazaiyi toh da ita? Yakamata tadawo shiyanason ganinta donhaka ya aika aka kira umma uwar soro, yace mata yaduba yayi nazari akan baiwar dayasa aka kora, ayi hakuri adawo masa da ita suna aiki da bilki yafi gane aikinsu. Ta amsa masa da toh, adaren ranar umma takira aliya tasanar mata bataji dadiba dontasan meyakesonyi, zaibata mata plans dinta, anma haka bayadda ta iya, dl bilki takai masa shayi ya juye mata akaya yace ta aiko dayan baiwan, tana isowa tafadawa aliya duk jikinta yabaci donma Allah yasa ba tafashashe bane balle yakoneta, aliya cikin dacin rai tanufi fanninsa bayan anmata iso sannan tashiga yana zaune akan kujera ta tsuguna tamika masa sannan yace dama ke baiwa ce kika fita? Da izinin waye? Kanta agefe tace "gimbiya falmata" yaja tsaki sannan yace "da mummyna kike aiki?" Yanzu zantona miki asiri kasheki zaayi baiwa dake kinfita kinje kina tonamana asirin gyda ko?" Batace komi ba, jiyayi kaman jikinsa na mararin jikinta, gashi yadan sha giyansa kadan, kanta yanufa tamike tana matsawa haka yakomota duk karfin datake jidashi yahadata yadama wurgata kan gado yayi yafara sumbatu, tana kokarin tashi yana kokarin danneta. Ganin zata masa taurin kai gashi ji yake zuciyarsa na masa zogi, na masa radadi kaman yarasa wani abu a fannin jikinsa yanzu yasamu baisan lokacin daya rinka naushinta ba tuni tayi laushi yakwanta luff ajikinta, tareda cewa nafiso injini haka. Aliya tagama galabaita batasan lokacin data gantsara masa cijo ba bashiri ya tsala kara tuni aka bude Kofan daki .
To be continue....
To subscribe for inside arewa story add 08066680993 on whatsapp for more updates.

No comments:

Post a Comment