Tuesday 12 June 2018

Shugabannin Yarbawa Na Ci gaba Da Jinjinawa Buhari Kan Baiwa Abiola Lambar GfCR

▪ Dole In Yiwa Buhari Yakin Neman Zabe A 2019 — Tinubu

▪ Buhari Ya Amince Da Baiwa Wasu 'Yan Siyasa Lambobin Yabo

Shugabannin Yarbawa na ci gaba jinjinawa Shugaba Muhammad Buhari bisa matakin da ya dauka na baiwa Marigayi M.K.O Abiola Babbar lambar girmamawa ta kasa wato, GFCR a yau a ranar 12 ga watan Yuni wadda rana ce da aka soke zaben Shugaban kasa da marigayin ya lashe a 1993.

Tuni dai, Tsohon Gwamnan Legas, Bola Tinubu ya tabbatar da cewa wannan mataki da Buhari ya dauka na girmama Abiola ya sa dole ya sadaukar da rayuwarsa wajen yi wa Buhari yakin neman zabe a shekarar 2019 inda ya nuna yin haka girmamawa ce ga daukacin Yarbawa.

Shi kuwa dan fitaccen lauyan nan Marigayi Gani Fawehenme wanda shi ma ya samu lambar girmamawa duk da yake a lokacin yana raye ya ki karbar lambar, Mohammed Fawehenme ya nuna cewa babu wani Shugaba a tarihin Nijeriya da ya san abin da ya dace irin Shubaga Buhari.

Haka nan kuma Shugaba Buhari ya amince da baiwa wasu Fitattun 'yan siyasa da suka taka rawa a dimokradiyyar Nijeriya lambar girmamawa. Da yake tabbatar da haka Sakataren gwamnatin tarayya, Boss Mustafa ya ce nan bada jimawa za a fitar da sunayen wadannan 'yan siyasar

Shugaba Buhari ya yabi matasan Najeriya a ganawar da yayi da firaiministan Morocco

Shugaban kasa, Muhammadu Buhari ya gana da firaministan kasar Morocco, Saadeddine Othmani, inda ya shaida mishi cewa mutanen Najeriya, wanda yawancin su matasa ne suna da kokarin aiki tukuru duk inda suka samu kansu a gida Najeriya ko a kasashen waje.

Shugaba Buhari ya kara da cewa shi yasa gwamnatin shi take kokarin ganin ta tallafawa matasan dan su bayar da gudummuwar data dace wajan ciyar da kasar gaba,

Ya kara da cewa Najeriya na kokarin ganin ta inganta harkokin Ilimi dana noma ta hanyar yin hadaka da kasashen Duniya wajan tabbatar da hakan.

Ya bayyana cewa an samu raguwar shigar da shinkafa kasar sosai, sannan kuma hadin gwiwar da Najeriya tayi da kasar Moroccon yasa kudin takin zamani ya ragu da kashi hamsin cikin dari.

Da yake jawabi a ganawar tasu, Firaiminista, Saadeddine ya bayyana cewa 'yan Morocco sun tabbatar da 'yan Najeriya nada hazaka dan sun gani a kasa, sannan kuma zasu cigaba da tabbatar da dangantaka me kyau da Najeriya.

Shugaba Buhari ya kuma gana da shugaban masu bayar da shawara akan harkar kasuwanci na kasar ta Morocco Ben Chemmas da kuma shugaban majalisar wakilai Habib El-Malki.

'Yan sanda sun tabbatar da mutuwar mutum 8 a arangamar da 'yan baranda su kayi da 'yan banga a Sakkwato

Hukumar Yan sanda reshen Jihar Sakkwato ta tabbatar da rasuwar mutane takwas a wata rikici da ya barke tsakanin yan baranda da yan banga a jiya Litinin a karamar hukumar Isa da ke Jihar Sakkwato.

Jami'ar hulda da jama'a ta rundunar, Cordelia Nwawe ta shaidawa yan jaridar cewa ana kyautata zaton mutane takwas ne suka rasu ciki har da wani dattijo da yan barandan su kayi kokarin sacewa.

Mrs.Nwawe ta kara da cewa har yanzu ana cigaba da gudanar da bincike a kan lamarin, ta kuma ce ana kyautata zaton yan barandan sun zo ne daga kauyukan jihar Zamfara da ke makwabtaka da Sakkwato.

Ta kuma ce kwamishinan Yan sanda na jihar ya ziyarci kauyen da abin ya faru don yin jaje ga iyalen wadanda abin ya shafa tare da tabbatar musu cewa yan sanda za su binciko wadanda suka aikata wannan laifin.

Sai dai a wani rahoton, an ce mutane 13 ne suka rasu sakamakon yunkurin da yan barandan su kayi na sace wani dattijo ranar Asabar a kauyen Dan Tasango a Gundumar Gebe.

A cewar wani ganau, yan barandan sun harbe dattijon ne saboda ya ki yarda su tafi dashi, hakan ne yasa yan bangan garin suka hada kai don bin sahun yan barandan.

Majiyar ta cigaba da cewa 'yan barandan sunyi wa yan bangan kwantar bauna a hanyar Kamarawa-Barafawa inda akayi musayar wuta inda yan barandan suka kashe yan banga bakwai su kuma aka kashe musu mutane biyar.

Sai dai yan barandan sun kwace gawawwakin mutane biyar din da aka kashe musu kamar yadda suka saba saboda kar a gane kosu wanene.

Monday 11 June 2018

Matashi Ya Yi Wa Budurwarsa Yankan Rago A Jihar Yobe

Ana zargin wani matashi dan garin Potiskum dake jihar Yobe mai suna Muhammad Isa Adamu da yi wa budurwasa mai suna Hauwa yankan rago.

A bisa bayanan da iyayen Hauwa mazauna garin Damaturu suka yi, sun ce a ranar 29/05/2018 Hauwa ta fita da safe da niyyar sayo biredi a shago mafi kusa da su, sai dai tun daga fitar ta ba ta dawo ba har zuwa yammaci, wannan dalilin ya sa suka bazama nemanta, yayin da suka bada cigiyar ta a gidajen rediyo da ma wajen 'yan sanda.

Kwatsam sai suka ji an samu gawar wata budurwa a kan titin Gujba, inda ba su yi kasa a guiwa ba zuwa wurin inda suka tabbatar da 'yarsu ce.

A yayin da wannan matashi yake karin haske akan abun da ya faru, ya shaidawa manema labarai a garin Damaturu cewa, ya gayyaci Hauwa tsohuwar budurwarsa wadda ya fara nemanta tun 2014, soyayyarsu tayi nisa sosai, kuma bai taba sa ta wani abu ta ki yi ba, ya tabbatar da irin biyayya da Hauwa take masa, wannan dalilin yasa da ya gayyace ta kan hanyar Gujba, ba ta yi masa jayayya ba.

A cewar sa, bayan sun gama hirar su da Hauwa, sai ya umarce ta da ta rufe idonta, ba ta yi jayayya ba nan take ta rufe idon ta ba tare da ta san me yake shirin yi mata ba, sai ya ciro wuka ya soke ta a wuya, bada wani bata lokaci ba rai ya yi halinsa.

Da aka tambaye shi ko mai ya yi zafi har ya yanke wannan danyen hukunci ga wadda yake so?

Sai ya ce, ya yi iya kokarin sa don ganin mahaifansa su je Damaturu su nema masa auren Hauwa amma sun ki, kwatsam sai ya ga wani matashi ya fara zuwa wajen ta, wannan dalilin ya sa ya yanke hukuncin kashe ta kowa ma ya rasa.

A bisa bayanan da kwamishinan 'yan sanda na jihar Yobe ya yi wa manema labarai, ya tabbatar da faruwar lamarin, ya kuma yi alkawarin nan bada jimawa ba za su gurfanar da wannan matashi gaban kotu dan yanke masa hukunci.

Barazanar Tsige Buhari Ta Jefa Dogara Cikin Jangwan

Shugabanni jam'iyyar APC na mazabar Shugaban Majalisar Wakilai, Yakubu Dogara sun cimma matsaya na maye gurbinsa da wani sabon dan takarar mai suna Godfrey Mannaseh bisa abin da suka kira adawar da Dogara ke yi da Buhari da kuma Gwamnan Bauchi.

Shugabannin uku, Haruna Rikaya, Malam Zubairu da Wakili Amadi sun nuna cewa Shugaban majalisar wakilan da na hannu kan barazanar da 'yan majalisar suka yi kwanaki na tsige Shugaba Buhari inda suka jaddada cewa ba irin wakilcin da suka tura shi ya yi masu ba kenan.

Shugaba Buhari Da Sarkin Moroco Sun Kulla Alaka Kan Harkokin Man Fetur, Gas Da Sauransu

Shugabannin biyu sun tattauna da kuma cimma yarjejeniya na karfara tattalin arzikin kasashen biyu.

Wadanda suka rattaba hannu kan wannan yarjejeniya sune Manaja a kamfanin NNPC, Mr Farouq da kuma ministan man kasar Moroco, Misis Amina Benkhadra

Haka kuma shugaba Muhammadu Buhari da Sarki Muhammad VI sun shaida yarjejeniyar gina babban masana’antar hada sinadarin takin zamani wato Ammonia, wanda shugaban sanya hannun jarin Nijeriya, Mista Uche Orji da Mista Mostafa Terrab na Moroco suka rattaba hannu.

An Nemi Buhari Ya Binciki Yadda Obasonjo Ya Mikawa Kamaru Yankin Bakassi

An Nemi Buhari Ya Binciki Yadda Obasonjo Ya Mikawa Kamaru Yankin Bakassi

Tsohon Gwamnan Abia, Orji Uzor Kalu ya nemi Shugaba Muhammad Buhari kan ya binciki Cif Olusegun Obasonjo game da yadda ya mikawa Kasar Kamaru yankin nan mai arzikin man fetur na Bakassi .

Tsohon Gwamnan ya ce, akwai wata manufa ta biyan bukata kansa idan aka yi la'akari da yadda Obasonjo ya mika yankin cikin sauki ba tare da wata jayayya ba.

Wasu Inyamurai Guda Biyar Sun Musulunta


Ga abinda Malama Aishat Obi 'yar kabilar Ibo dake da'awar jawo 'yan uwanta Inyamurai cikin addinin musulunci ta rubuta a shafi ta na facebook:

"Allahu Akbar, Asalamu alaikum 'yan uwana musulmai maza da mata. Ku taya ni murnar shigowar wasu 'yan yankunan kudu maso kudu da kudu maso gabashin kasar nan cikin addinin musulunci a jiya a garin Fatakwal.

Sunayen su sune kamar haka:

(1) Believe Isaiah (Sehid Isaiah)  (daga jihar Rivers)

(2) Okechukwu Onwusaraka (Isan Onwusaraka) (daga jihar Imo)

(3) Chinonso Onyejiako (Hassan Onyejiako) (daga jihar Imo)

(4) Ngozi Uwa (Nafisa Hassan) (daga jihar Imo)

(5) Oluchi Eze (Khadija Eze) (daga jihar Imo)

Malama Aishat Obi ta kuma yi fatan Allah ya kare ta tare da ba ta nasara a da'awar da take yi don ganin ta jawo 'yan uwanta Inyamurai cikin addinin Musulunci.

Friday 8 June 2018

Zan Bada Kyauta Mai Tsoka Ga Duk Wanda Ya Nuna Mini Aikin Da Buhari Yayi Cikin Shekaru Uku—Tanko Yakasai

Zan Bada Kyauta Mai Tsoka Ga Duk Wanda Ya Nuna  Mini Aikin Da Buhari Yayi Cikin Shekaru Uku—Tanko Yakasai

Shugaban Majalisar Dattawan Arewa, Alhaji Tanko Yakasai ya kalubalanci kowane ne kan a nuna masa aiki guda da Shugaba Muhammad Buhari ya kammala a cikin shekaru uku da ya yi kan mulki.

Ya kara da cewa mutane nawa ne aka yankewa hukunci bisa tuhumar rashawa a shirin yaki da rashawa da Shugaban ya kaddamar inda ya nuna cewa har yanzu Buhari ya kasa hukunta tsohon Sakataren gwamnatin tarayya Babachir Lawal wanda aka samu da laifin rashawa dumu-dumu.

Bincike : Matafiya da kafa da sauri,sun fi tsawon rai

Bincike : Matafiya da kafa da sauri,sun fi tsawon rai

Sakamakon wani sabon bincike da aka wallafa a makalar  "MotsaJiki"  ta kasar Ingila,ya nuna alakar da ke tsakanin tafiya da kafa da sauri-sauri da kuma tsawon rai.

Masana a kasashen Burtaniya da Ostireliya sun sanar da cewa, yawancin wadanda ke tafiya da kafa a gaggauce,basa kamuwa da ciwon zuciya.

Da wannan dabarar,hatsarin kamuwa da ciwon zuciya wanda a yawancin lokaci shi ne ummal-aba'isar mutuwar masu sama da shekaru 60,na raguwa da kaso 53 cikin dari.

Masu bincike sun gano cewa,tafiya da kafa da sauri tsawon awanni 5 zuwa 7 sun isa matuka gaya ga masu bukatar suyi rayuwa lami-lafiya.

Manufar wannan tafiyar ita ce,  bai wa zuciya damar bugawa da gaggawa,shi yasa kamata yayi a dinka takawa da sauri ta yadda za a yi kankanuwar zufa.

Masanan na Burtaniyar sun sanar da cewa, motsa jiki tsawon dakiku 30 a kowace rana da kuma cin lafiyayyen abinci, na tsawaita raywuwar mutum da shekaru 10.

Ya zama wajibi Allah ya jarrabci jihar Zamfara da masifu da bala'o'i daban daban

Ya zama wajibi Allah ya jarrabci jihar Zamfara da masifu da bala'o'i daban daban,

kamar kisan jama'a da garkuwa da mutane da suka zama ruwan dare yanzu a fadin jihar.

Magidanta na zina Matan aure na zina, samari na zina 'yan mata na zina, wasu mazan na luwadi wasu Mata na madigo, wasu na lalata da Mata mahaukata, wasu na bin dabbobi da lalata, ana satar jarirai ana yankawa, wasu na zuwa makarbarta suna tono gawawwaki ana cire wasu sassa na jikinsu domin tsafi, 'ya'ya na bijirewa iyayen su, da sauran manyan laifuka da ake aikatawa ba dare ba rana a Zamfara, wallahi dole Allah ya fitini jihar Zamfara, Allah mun tuba!!! ~ Inji Dakta Tukur Sani Jangebe a yayin karatun tafsirin kur'ani mai girma da yake gabatarwa a Massalachin GRA Gusau jihar Zamfara.

Tsaffin ‘yan sabuwar PDP zasu fice daga APC 23 ga watan Yuni

Wata majiya mai tushe ta shaidawa gidan jaridar DAILY TRUST cewar nan da ranar 23 ga watan Yuni tsaffin ‘yan sabuwar PDP da suka hada da SHugaban majalisar dattawa dBukola Saraki da kakakin majalisar wakilai na tarayya Yakubu Dogara zasu fice daga jam’iyyar APC zuwa wata jam’iyya.

Tsaffin ‘yan sabuwar PDP din sun zabi ranar 23 ga watan Yuni ne, domin ta zamo daidai da ranar da jam’iyyar APC zata yi babban taron ta na kasa inda zata zabi sabbin Shugabanni.

Majiyar ta shaidawajaridar cewar jiga jigan jam’iyyar sun gama tattara komatsansu domin ficewa daga jam’iyyar ta APC domin tsallakawa zuwa jam’iyyar adawa wanda suke karkashin jagorancin Alhaji Kawu Baraje.

Idan har ta tabbata tsaffin ‘yan sabuwar PDP zasu fice daga jam’iyyar APC a ranar babban taron jam’iyyar na kasa, to, tarihi zai maimaita kansa. Domin a shekarar 2013 ne tsohon mataimakin Shugaban kasa Atiku Abubakar ya jagoranci wasu Gwamnoni da mukarraban PDP suka ficee daga jam’iyyar a lokacin da jam’iyyar ke yin babban taron ta na kasa.

Inda bayan ficewarsu daga jam’iyyar PDP suka hallara a Shehu YarAdua santa inda suka bayyana kansu a matsayin sabuwar PDP, karkashin jagorancin Alhaji Kawu Baraje wanda ya jagorance su a lokacin.

Ficewar da tsaffin ‘yan sabuwar PDP suka yi daga jam’iyyar tasu, na daga cikin dalilan da suka sabbabawa jam’iyyar ta PDP samun koma baya tare kuma da faduwa babban zaben shekarar 2015.

Thursday 7 June 2018

Uwar Nakasassu da Marasa Galihu na Jihar Kaduna , Hajiya Hadiza El-Rufai ta Sha Ruwa da Mata Nakasassu.

Uwar Gidan Maigirma Gwamnan Jihar Kaduna, Hajiya Hadiza El-Rufai wanda ake yi wa lakabi da “Uwar Nakassu da Marasa Galihu” yau Alhamis 7 ga watan Yuni, 2018 ta kira mata nakasassu da marasa galihu na Jihar Kaduna a nan Gidan Gwamnati na Sa Kashim Ibrahim da ke Kaduna don shan ruwa tare da su.

Hajiya Hadiza El-Rufai takan kira wadannan masu bukata ta musamman ne shan ruwa don nuna musu irin yadda Gwamnatin Jihar Kaduna ta damu da su. Wannan dalilin ya sa duk shekara ita uwar gidan gwamnan kan kira su Shan ruwa, sannan har ta ba su atamfofi don su je su dinka su sami kayan sallah.

A jawabin Kwamishinan Mata da walwalar Jama’a, Hajiya Hafsat Baba ta bayyana wa wadannan mata nakasassu, Gwamnatin Jihar Kaduna na nan tana gyarawa da gina sababbin cibiyoyi na koyar da nakasassu sana’o’i a mazabu uku da ke fadin jihar don su da ‘ya’yansu su zama masu dogaro da kai.

Sannan ta bayyana yadda Gwamnatin Jihar Kaduna ta dauki daya daga cikin wadannan mata nakasassu aka ba ta mukami na P.A a ofishinta duk dai don nuna wannan gwamnati ta damu da su.

Su ma a nasu bangaren, wasu daga cikin nakasassun sun bayyana irin jin dadinsu yadda wannan gwamnati ta damu da su, wanda ba a taba nuna musu irin wannan kaunar ba a gwamnatocin baya.

A Nuna Mani Aiki Guda Da Buhari Ya Kammala A Shekaru Uku—Tanko Yakasai


Shugaban Majalisar Dattawan Arewa, Alhaji Tanko Yakasai ya kalubalanci kowane ne kan a nuna masa aiki guda da Shugaba Muhammad Buhari ya kammala a cikin shekaru uku da ya yi kan mulki.

Ya kara da cewa mutane nawa ne aka yankewa hukunci bisa tuhumar rashawa a shirin yaki da rashawa da Shugaban ya kaddamar inda ya nuna cewa har yanzu Buhari ya kasa hukunta tsohon Sakataren gwamnatin tarayya Babachir Lawal wanda aka samu da laifin rashawa dumu-dumu.

Wednesday 6 June 2018

Tsige Buhari za mu yi tunda dai shi ba Allah bane – Hon.Jagaba Adams

Rahotanni sun nuna cewa wani dan majalisar wakilai, Jagaba Adams Jagaba ya caccaki gwamnatin shugaban kasa Muhammadu Buhari.

A cewar dan majalisar, babu wani abu da ake fuskanta a wannan mulkin baya ga bakar wahala da matsananciyar yunwa.

Jagaba ya kasance dan majalisa mai wakilatar Kachia da Kagarko na jihar Kaduna.

Furucin dan majalisar na zuwa ne bayan da majalisar dokokin kasar tayi barazanar tsige shugaba Buhari idan har bai aiwatar da kudurorin da suka zartar ba.

Mista Jagaba ya ce idan har Shugaba Buhari bai aiwatar da kudurorin da suka bukata ba to za su tsige shi a bisa tsarin kundin mulkin kasa.

Jagaba ya jadadda cewa basa dari-dari akan yiwuwar hakan saboda

"Buharin ba Allah ba ne kuma bai yi kama da Annabi ba, duk inda ya yi kuskure za mu take shi" .

Buhari Ma Ya Ci Kudin Makamai, Cewar Sule Lamido

...idan Buhari ya kama Jonathan sai sama ta fado, cewarsa

Tsohon gwamnan jihar Jigawa, Dakta Sule Lamido ya zargi shugaban kasa Muhammadu Buhari da cewa shi ma yaci kudin makamai.

Lamido ya bayyana haka ne a shafinsa na kafar sadarwar zamani, Facebook, inda yace tsohon mai baiwa tsohon shugaban kasa Goodluck Jonathan shawara kan harkokin tsaro, Kanau Sambo Dasuki ya baiwa Buhari motoci masu sulke guda biyu bayan da Boko Haram ta kai masa hari a Kaduna.

Haka kuma Sule Lamido ya kara da cewa me ya sa Buhari ya gagara kama Jonathan, bayan duk wadanda ake tuhuma suna na da nasaba da tsohon shugaban?

“Wai a ina Dasuki ya samu dala biliyan 2.5 da ya rarrabawa manyan mutane yayin da ake gab da zaben 2015, laifin da ya sa har yanzu yake daure a hannun hukumar DSS? A ina Nenadi ta samu makudan bilyoyi da ta rarrabawa jihohi wanda ya sa a yanzu haka take gaban Kotu?

“Ga amsa, dukkaninsu sun samu kudaden ne daga babban bankin Nijeriya dake karkashin shugaban bankin na yanzu, Godwin Emefeile, kuma tsohon shuhgaba Jonathan ne ya bada wannan umarni", cewar Lamido.

Daga karshe Sule Lamido wanda yake  takarar shugaban kasa a jam’iyyar PDP yace: “Don haka tunda Alkali Binta Nyako ta yanke hukucin cewar bai kamata a kama duk wanda aka basu umarnin yin laifi ba, Gwmanatin Buhari ba zata iya kama Jonathan bane, ta gwada mu gani, da sai sama ta fado".

Shekaru Hudu Masu Albarka Akan Karagar Masarautar Gombe

Daga Haji Shehu

Tun bayan dalewarsa kan karagar mulki. Mai martaba sarkin Gombe Dr. Abubakar Shehu Abubakar lll, yazamto zakaran gwajin dafin sarakuna a fagen tallafawa talakawan jaharsa ta fuskoki daban daban ba tare da gajiyawa ba Dare, Rana, Ruwa, da ma iska basu katsewa mai martaba cigaba da shimfida ayyukan alkairi ga talakawan jahar Gombe ba.

Halinsa na jinkan talakawa yasa mai martaba Abubakar Shehu Abubakar lll ya kirkiro wata gidauniya wacce zatake tallafawa mabukata musamman talakawa, marayu, marasa galihu da sauran su, gidauniyar mai suna SHEHU USMAN ABUBAKAR FOUNDATION wacce akayiwa lakabi da sunan marigayi sarkin Gombe Dr. Shehu Usman Abubakar Allah ya jikanshi, ta cigaba da daura ayyukan alkairi karkashin jagorancin mai martaba sarki.

Shehu Usman Abubakar Foundation wacce aka kirkito ta a watan Feburairu na alif 2015 ta cimma ayyuka daban daban don inganta rayuwar talakawa da marasa galihu. Sati biyu da kafa wannan gidauniya, gidauniyar ta rarraba manyan motocin abinci guda biyar ga talakawa da marayu don inganta walwalar su.

A watan Yuli na 2015, gidauniyar ta tallafawa fiye da matasa 200 shiga makarantar gaba da secondary ta hanyar biya musu kudin rijista.

A watan azumi, tawagar gidauniyar karkashin jagorancin shugabanta Mai Martaba sarkin Gombe Abubakar Shehu Abubakar lll sunkai ziyarar duba marasa lafiya a asibitin koyarwa na Gomnatin tarayya dake Gombe (FED. TEACHING HOSPITAL) da kuma asibitin kwararru mallakan jahar Gombe (SPECIALIST HOSPITAL), inda suka bawa kowane majinyaci Naira dubu 5000 don shan ruwa. Tawagar bata tsayaba saida ta fadada ziyarar zuwa masallatai tare da rarraba kayan abinci ga mabukata.

A watan Satumba 2015, Gidauniyar ta duba kiraye kirayen al'umma na neman a samar musu da ruwan sha, nan take gidauniyar tayi azama ta bada kwangilar tonon famfunan burtsatsai guda 21 a unguwanni da kuma sansanonin yan gudun hijira don samun saukin wahalhalun ruwan sha.

A watan October/November 2015, gidauniyar tayi bikin da ya sosawa dubun dubatan jama'a rai, domin kuwa gidauniyar ta karrama yara marayu da marasa galihu tayi ta hanyar daukan nauyin karatun yara fiye da 1500 daga firamare harzuwa jami'a.

Gidauniyar bata tsaya nan ba domin a watan November 2015 ta leka zuwa gidan yarin dake jahar Gombe, namma ta yanta fursunoni guda 61 sannan ta koyar musu sana'a don kaucewa sake afkuwar abunda yafaru da su abaya.

A watan December ta 2015, gidauniyar ta samo kwararrun likitotin ido don yiwa majinyata 21 aikin ido kyauta

Gidauniyar ta tallafa da kashi 30% na kudin abincin mai gina jiki da ake ciyarda yara kankana masu duke da ciwon HIV, a wajen wani biki da hukumar dake yaki da yaduwar cutar HIV na jahar Gombe mai suna GOMSACA ta shirya.

Gidauniyar tare da hadin guiwar kamfanin Media trust LTD sun rarraba kayakin abinci da na aikace aikacen gida na zunzurutun kudi har naira miliyon 5000000 ga yan gudun hijira a jahar Gombe.

Gidauniyar bata tsaya nan ba saida ta tallafawa almajirai kimanin dubu 26000 daga makarantu 333 da buhu hunan abinci taburmai da kuma littatafa na karatu.

Ruwan Sama Da Iska Mai Karfin Gaske Ya Jawo Asarar Dukiyoyi A Jihar Kebbi


Barnar ruwan sama da iska mai karfi sun yi barna a kauyen Kambaza na karamar hukumar Mulkin Gwandu, inda aka yi asarar dukiya mai dibin yawa da kuma rushewar gidaje, kuma jama'a da dama sun samu raunuka. Sai dai babu asarar rayuwa, sannan mutane da dama sun rasa matsugunnansu.

Daga Zaidu Bala Kofa Sabuwa, Birnin Kebbi

Tuesday 5 June 2018

Tsuguno bata karewa Dino Malaye ba za'a cigaba da gurfanar dashi gaban Kotu


Tunda Dino Melaye ya samu lafiya, a cigaba da gurfanarsa – AGF Malami ya bukaci kotu

Naijdotcom ta ruwaito Ministan Shari’a kuma babban lauyan tarayya, Abubakar Malami, ya bukaci babban kotun birnin tarayya Abuja, da ta cigaba da gurfanar da Sanata Dino Melaye, bayan dakatad da sanadiyar jinya da yake yi.

Jaridar Punch ta bada rahoto a jiya Litinin cewa ta samu wasikan da aka turawa kotu tana sanar da ita cewa Dino Melaye ya samu lafiya har ya koma bakin aiki a majalisar dattawa ranan30 ga watan Mayu.

Ofishin babban lauyan kasa tana tuhumar Dino Melaye da karya ga hukumar yan sanda domin yiwa na kusa da gwamnan jihar Kogi, Edward Onoja David, sharri cewa ya tura wasu kashe shi.

A ranan 17 ga watan Mayu 2018, Justice Olasunbo Goodluck, ya dakatad da karar Melaye ne zuwa lokacin da za’a sallameshi daga babban asibitin tarayya da ke Abuja inda yake kwance.

A wasikar, lauyan gwamnati, Mr Shuaibu Labara, ya laburtawa kotu cewa an salami Melaye kuma ya koma bakin aiki rike da sanda da abu a wuya.

Tunda ya koma kuma, an ganshi yana magana a majalisa saboda haka, kotu ta bada sabon ranan domin cigaba da gurfanarsa.

Gwamnatin Jonathan ba ta yi kama karya irin ta wannan Gwamnain ba – inji Dakta Gumi

Daga DailyNigerian Hausa

Fitaccen malamin addinin Musuluncin nan,Sheikh Dr. Ahmad Abubakar Mahmud Gumi ya caccaki rundunar ‘yan sanda ta kasa kan yadda suka ci zarafin Shugaban majalisar dattawa Bukola Saraki. A cewarsa cin fuska ne ‘yan sanda su gayyace shi maimakon su je su same shi.

Mutum na uku a kasar nan yana da matukar muhimmanci kwarai da gaske, bai kamata ba kuma a wulakanta shi ba, irin yadda ‘yan sanda suke yi masa yanzu haka. Idan Shugaban kasa ya bari aka wulakanta shi, to ya sani kansa ya wulakanta”

“Idan aka dore a haka, to, shima Shugaban kasa duk ranar da ya sauka haka zai kare ba shi da kima, ana iya sanya ‘yan sanda su kama shi ko su wulakanta shi babu kuma abinda zai faru”

“Me yasa ake tsare da Sambo Dasuki, ku gaya mana a lokacin Gwamnatin Jonathan da ta gabata an yihaka ne? Amma me yasa yanzu ake yiwa mutane bitada da kulli bayan a zamanin gwamnatin Jonathan sam bamu shaidi hakan ba”

Anci zarafin addinin Musulunci a wakar Shaku Shaku – MURIC


Daga DailyNigerian Hausa

*Wakar fitsarar da aka ci zarafin addinin Musulunci*

Wani mawaki da ake kira da sunan Folarin Falana ko inkiya (Falz the Bahd Guy) ya fitar da wata sabuwar waka mai suna Shaku Shaku da yaci zarafin Fulani da kuma addinin Musulunci a cikinta.

A cikin faifan bidiyon wakar an nuna wani Bafulatani yana sare kan mutane babu gaira babu dalili, abinda yake nuna cin zarafi ga kabilar Fulani a Najeriya. haka kuma a cikin akar an ci zarafin addinin Musulunci, inda aka nuna wata mata sanye da Hijabi tana rawar ‘yan kwaya.

Wakar dai an sanya mata sunan “This is Nigeria” ma’ana “Wannan ita ce Najeriya” inda a cikin wakar aka dinga wata rawa ta rashin mutunci da aka sanya sunan shaku shaku.

A sabpda haka ne itacciyar kungiyar kare ‘yancin Musulmi ta MURIC ta yi Allawadai da wannan sabon faifan bidiyo da ya ci zarafin Musulmi, ta nemi kuma a gaggauta janye wakar daga kasuwa matukar ana son zaman lafiya.

Ta Ya Za A Magance Karuwar Zubar Da Ciki Ba Bisa Ka’ida Ba?

Tsoro da abin kunya da buna kyama ya sanya miliyon mata tsunda zubar da juna biyu harda yin hakan ba’ a bisa ka’ida ba, inda suke zuwa harmatattun asibiti don su zubar da juna biyun da suka dauka  kuma hakan yana jefa rayuwar su da lafiyar su a cikin hadari.

A wannan rahoton da SADE OGUNTOLA ta rubuta kuma ABUBAKAR ABBA ya fassara, kwararru akan harkar kiwon lafiya sun bayyana cewar, kaucewa mutuwar masu zubar da ciki ba’a bisa ka’ida ba, za’a iya samun nasara hakan ne idan irin wadannan matan sun kula da ‘yancin su yin jima’i da kuma kula da kiwon lafiyar  su.

Lokacin da ‘yan fashi da makami suka yiwa wata Mildred Haruna (wanda wannan ba shine sunanta na ainahi ba) fyade, a anguwar su dake cikin jihar Legas a shekarar 2005, ba ta taba tsammanin fyaden da aka yi mata da daren ranar ba zaici gaba da rikitar mata da rayuwar ta ba.


Bayan dimautar data tsinci kanta bayan yi mata fyaden, Mildred ta gano cewar, ta samu juna biyu kuma dimautar tata, taci gaba da karuwa saboda, duk da shawarar data yanke na ta bar juna biyun, sai dai dan albashin da take karba ba zai iya ba ta sukunin daukar dawainiyar abinda zata haifa ba.

Sannan kuma mutane za su dinga kallon abinda zata haifa a matsayin shege tunda baida uba. Sai dai, taga abinda yafi mata mafita shine ta zubar da cikin amma sai dai ba abu ne mai sauki a gare ta ba domin kuwa, maganar zubar da ciki abu ne da ya kamata ayi shi a asirce. Ta yanke shawarar zuwa asibiti don ta yiwa likita korafin ba ta da lafiya yadda zata ja hankalin likitan.

Amma ba za ta yi korafin jin tabin hankali ba ko nuna akawai damuwa tare da ita ba saboda jaririn dake cikinta yana ci gaba da kara girma, inda a karshe dai ta haifi abinda ke cikinta. A wata sabuwa kuma, wata ‘yar shekara ashirin da biyu mai suna Comfort, wadda dalibace a jami’a, itama an dirka mata ciki.

Sakamakon cikin, ta shiga cikin rudani da jin tsoro akan abinda zaije yazo, inda daga baya ta yanke shawar zubar da cikin ta hanyar zuwa gun likitan bogi. Sai dai, ta samu nasarar zubarda cikin, amma daga bisani ta fara jin zafi wanda ya janyo mata ta fara kwarar da jini an kuma yi gaggawar kaita Asibiti daga bisani da ta mutu.

Hukumar Lafiya ta Duniya (WHO) ta bayyana cewar an samu kimanin miliyan ashirin da biyar na zubar da ciki ba bisa ka’ida ba da aka kiyasta ya faru a fadin duniya dukkan shekara, musamman a kasashen masu tasowa. Daga cikin wannan adadin, miliyan takwas na zubar da cikin, anyi su ne ba bisa ka’ida ba ko kuma a cikin wasu yanayi masu hadarin gaske. Bugu da kari, yawan  zubar da cikin da aka yi ba a bisa ka’ida ba, ya faru ne a nahiyar Asia kuma uku daga cikin hudu na zubar da cikin, ya auku ne a nahiyar Afirika da Latin Amurka.

Zubar da cikin da aka yi ba’a bisa ka’ida wanda har ya janyo mutuwa, yafi yawa a Afirika. Ganin irin tunanin mafi yawancin ‘yan mata da kuma mata da suka dauki cikin da basu shirya ba, kwararru akan kiwon lafiya sunyi imanin cewar, zubar da ciki ba a bisa ka’ida ba yana kara zama babbar matsala akan harkar kiwon lafiya, musamman a kasashen da masu  karamin karfin tattalin arziki, harda Najeriya. Maganar gaskiya, jin tsoro da fadawa a cikin abin kunya da nuna kyama sune ke jefa miliyoyin mata zuwa Asibitocin boji don a zubar masu da cikin ba’a bisa ka’iba, inda hakan ke shafar lafiyar su da kuma rayuwar su kuma matan sune suke jin jiki in hakan ta faru gare su a kowanne lokaci.

Ana samun zubar da ciki ba ‘a bisa ka’ida ba idan wanda zaiyi aikin zubar da cikin  baida wata kwarewa ko kuma a Asibitin da bai cika sharuddan zama Asibiti ba ko kuma dukkan biyun. Abin takaici, nuna kyama ga matan da suka samu ciki ba tare da yin aure ba ko kuma a tsakanin ‘yan mata, ya kan sanya su fada a hannun likitocin bogi, inda hakan yake janyo masu ziyartar kabari ba tare da sun shirya ba. Ba kowa wacce mace data sanu ciki ba tare da aure ba, takan kasance abin nunawa a gari.

A cewar wata Darakata ta Ipas Hauwa Shekarau tace,”sai dai mutane baza su samu cikakken labarin ba.” Ipas kungiya ce mai zaman kanta da take gudanar da ayyukan kiwon lafiya a fadin duniya da kuma tabbatar da mata suna zubar da ciki a bisa ka’ida da samar da magunguna. Shekarau ta bayyana hakan ne a wani taron bita na kwana uku da tsare-tsare data shiryawa ‘yan jarida.

A cewar ta,“za su sanar da masalaha ga abokin wanda zai samar masu da hanya mafita, amma wadanda za su jagorance su zuwa ga zubar da ciki ba a bisa ka’ida.”

Shekarau taci gaba da cewa, sai dai abin takaici, damuwa ta zubar da ciki tanada yawa dake hana mutane akan daukar matakan da ya dace.” A cewar ta,“tunda basu san komai ba a zahiri, suna kawai dauka maganar kamar ba wata illa bace.” Ta yi nuni da cewa “wannan shine yake haifar da fadawa ga hannun likitocin bogi  da rashin samun kulawa na kiwon lafiya da ya dace.” Tace, illolin zubar da ciki ta hada da, zai iya janyo cutar cancer ta nono kuma matar data zubar da ciki ya kai har sau hudu, zatafi saurin mutuwa haka yin amfani da magunguna don a zubar da ciki zai iya janyo cutar (menopause). Bugu da kari, hana samun damar zubar da ciki, itace hanyar da tafi dacewa wajen rage zubar da ciki kuma idan mace tana zubar da ciki zai hana mata haihuwa saboda wasu sassan dake cikin jikinta za su lalace.

Ta bayyana cewar “kuma wani abin takaici, kin bin ka’ida wajen zubar da ciki ba wai kawai yana shafar yawan zubar da ciki bane, yana kuma hana cimma burin da ake bukata.“

Ta yi nuni da cewa, mafi yawancin kama  masu zubawarwa da mata ciki da aka yi  suna karewa ne a kotu kuma ba’a yanke masu hukunci, sai dai idan wadda aka zubarwa da cikin ta mutu ko kuma wata illa ta same ta.” A cewar ta, miliyan 1.25 na zubar da ciki da akeyi a duk shekara, ya faru ne a Najeriya a shekarar 2012 a bisa binciken da ciniyar Guttmacher ta gudanar. Wannan adadin, kamar a tsoma Allura ce a cikin ruwa sakamakon wani bincike da wani Asibiti ya gudanar a cikin jihohi sha takwas a Najeriya.” Yawan karuwar zubar da ciki ba ‘a bisa ka’ida yana da yawan gaske.

Sai dai, ta koka da akan tsar-tsaurar dokar da shugaban kasar Amurka Donald Trump ya dauka a fadin duniya, inda tace, hakan zai kara nuna kyama akan zubar da ciki domin hakan zai kara sanya illa akan binciken da kungiyoyi suke yi akan shirin lafiyar mata a nahiyoyin. Tsarin garin Medico da aka sani na doka ya rufewa kasar Amurka bayar da kudi ga kungiyoyi masu zaman kansu wanda suke gudanar da aikin da ya shafi zubar da ciki ko bayar da shawarwari ko kuma kare ‘yancin mata na daukar juna biyu.

A cewar Shugaban kungiyar gangamin kayyade iyali Dakta Ejike Orji, zubar da ciki ba ‘a bisa ka’ida ba yana faruwa ne sakamakon nauyin tattalin arzikin kasa. Orji ya zayyana illolin dake tattare da zubar da ciki ba’a bisa ka’ida wadanda kuma ya ce sune suka janyo hana daukar ciki a Najeriya. Ya ce, “akwai rashin jin dadi ga magidantan da basu iya daukar ciki, ya kara da cewa, a maganar gaskiya, mace musamman wadda ba ta iya daukar ciki ‘yan uwan nijinta sukan jefata a cikin damuwa.

” Dakta Orji ya ce koda yake, a kalla ga dukkan mata biyar da suke zubar da ciki ba’ bisa ka’ida ba, daya na iya mutuwa, kuma akwai wasu illolin dake biyo baya in sunyi hakan kuma akwai tsada sosai sakamakon kamuwar da matan suka yi da illolin zubar da cikin a yayin yi masu magani. Babban abinda yafi yi janyo barazana wajen zubar da ciki a bisa ka’ida, yana haifar kwararar jini da kamuwa da kwayoyin cuta da jin rauni a cikin sassan dake jikin matan.

A cewar sa, tsadar kudin da ake kashewa wajen samar da lafiya sakamakon matsalolin da suka auku a yayain zubar da ciki ba’a bisa ka’ida ba, yana zama nauyi ga harkar kiwon kafiya a tsakanin kasashe masu tasowa. Ya yi nuni da cewar “amma za’a iya magance wannan tsadar ta zubar da cikin idan an rugumi hanyar kayyade iyali data kamata.” Ya bayyana cewa, zubar da ciki wani abu ne mai wahalar gaske kuma abin tausayi da mutane suke ganin wani abu ne na rashin ‘yanci. Shi kuwa Mista  Edoza Obiawe wanda shima yake aiki a IPAS, “ya ce, samun ‘yancin daukar ciki wani abu ne na ‘yancin dan adam. Samun wadatacciyar tarawa da ingantaciyyar kiwon lafiya sun hada da; samar da magunguna na zamani da kula da zubar da ciki ko kuma karewa kamuwa da kwayar cutar kanjamau, wasu abu ne da za su taimaka wajen cimma burin ci gaba.

” Ya yi nuni da cewa, hanawa mata sararin zubar da ciki musamman idan akwai barazana ga rayuwar mata da suka dauki ciki, ko kiwon lafiyar su ko kuma idan cikin an same shine sakamakon fyade zubar sa cikin  ya sabawa ‘yancin dan adam. A karshe ya ce,” idan ‘yan mata suna da koshin lafiya suna kuma da ‘yancin su, za su kuma  iya zuwa makaranta don su koyo wasu dabaru don kula da lafiyar su yadda za su zama manya da aka tallafawa.”

Daga Leadship Hausa

Sanatoci da yan majalisar dokoki sun yanke shawarar tsige Buhari muddin bai cika sharudda 10 ba

DA DUMI DUMI: Sanatoci da yan majalisar dokoki sun yanke shawarar tsige Buhari muddin bai cika sharudda 10 ba

Naij.com ta ruwaito Yan majalisan wakilai da dattawa sun lashi takobin tsige shugaba Muhamadu Buhari face ya cika wasu sharruda goma da suka kindaya masa.

Bayan ganawar da yan majalisan sukayi a yau wanda ya kwashe akalla sa’o’I 4, yan majalisan sun yanke shawaran cewa za su tsige shugaban da karfinsu idan har bai cika wadannan sharruda 10 ba.

Sharrudan sune,:

1. A baiwa hukumomin tsaro umurnin kawo karshen kashe-kashen da ke faruwa a fadin kasa.

2. Cin mutuncin yan adawan da fadar shugaban kasa keyi ya isa hakan kuma kada ya sake faruwa

3. Wajibi ne bangaren zantarwa su bi doka

4. Za’a daurawa shugaban kawa alhakin dukkan abinda wadanda ya nada suka yi

5. Gwamnatin tarayya ta nuna gaskiya wajen yaki da rashawan da takeyi

6. Wajibi ne a karewa majalisar dokoki hakkinsu kuma ayi binciken wadanda suka sace sandar majalisa

7. Majalisar dokoki za ta hada kai da majalisar ECOWAS, EU,UN da yan kungiyoyin fafutuka wajen kare demokradiyyan Najeriya

8. Wajibi ne a kawo karshen rashin aikin yi a Najeriya

9. Wajibi ne a ja kunne kuma a caccaki sifeto janar na hukumar yan sanda

10. Wajibi ne a jinjinawa shugaban majalisan dattawa, Bukola Saraki da kuma kakakin wakilai, Yakubu Dogara.

Yan majalisan sunce face an cika wadannan sharruda, ba zasu dagawa bangaren shugaban kasa kafa ba.

Sunday 3 June 2018

Cigaba Da Tsare Zakzaky Tsagwaron Rashin Adalci Ne ~ Inji Buba Galadima

Tsohon babban na hannun daman shugaban Kasar Najeriya Muhammadu Buhari kuma fitaccen dan adawar cikin gida Injiniya Buba Galadima ya bayyana cewa
cigaba da tsare jagoran 'yan shi'a a Najeriya Ibrahim Zakzaky da gwamnatin tarayya ke cigaba dayi a matsayin rashin adalci tsagwaron sa.

Injiniya Buba Galadima ya bayyana hakan ne a yayin da ake tattaunawa da shi a gidan talabijin din nan mai zaman kan sa na AIT a wani shiri da ake cewa "Focus Nigeria: Matters Arising"
A lokacin da aka tambaye shi ra'ayin sa game da cigaba da tsare shi.

Wata ma'aikaciyar gwamnati ta rasa aikinta bayan sukar Osinbajo da Aisha Buhari

Wata mace 'yar Najeriya, Bolouere Opukiri ta rasa aikin ta mako daya bayan ta yi suka a kan mataimakin shugaban kasa Farfesa Yemi Osinbajo da uwargidan shugaban kasa Muhammadu Buhari, Aisha a dandalin sada zumunta na Twitter.

A ranar 5 ga watan Yulin shekarar 2017, Opukiri ta ayyana cewa Osinbajo 'Dan koyo' ne saboda a kwanakin baya ya yi tafiya zuwa kasar waje a yayinda shugaba Buhari ke birnin Landan duk da cewa ana samun rashin jituwa tsakanin fadar shugaban kasa da majalisa a wannan lokacin.

Wasu Sanatocin Najeriya sunyi suka a kan tafiyar ta Osinbajo kwana daya kafin matar tayi nata sukar, Sanata Enyinnaya Abaribe na jihar Abia ya ce tafiyar ta Osinbajo ta bar wani 'gibi' da ya dace shugaban majalisa Bukola Saraki ya cike ta.

Kazalika, ta kuma sake yin wani rubutu a Twitter kwanaki biyar bayan na farkon inda ta soki Aisha Buhari da cewa ta fiye kwakwazo a kan wasu daga cikin 'kuraye' da 'dila' da kusanci da mijinta inda ta ke kokarin nuna cewa Aisha Buhari ba ta da wayewa irin ta tsohuwar matar shugaba Jonathan wato Patience.

Wasu 'yan Najeriya masu kishin gwamnatin Buhari sun tattara wannan rubuce-rubuce guda biyu da ma wasu da suka biyo baya kuma suka aike da shi zuwa ga ofishin yada labarai na shirin yin afuwa ga masu tada kayan bayan Neja Delta inda Opukiri ke aiki don daukan mataki.

Ofishin ya yi nazari a kan rubuce-rubucen tare da yin wasu bincike kuma daga baya ya yanke shawarar korar Ms Opukiri inda suka ce abinda ta yi ya sabawa dokokin aikin gwamnati kuma barazana ce ga tsaron kasa.

Ms Opukiri ta shaida wa Premium Times cewa korar da akayi mata ba bisa ka'ida bace kuma an tauye mata hakkin bayyana ra'ayinta inda ta ce tabbas za ta garzaya kotu don a bi mata hakkin ta.

Saturday 2 June 2018

Iya Tsawon Rayuwa Ta Ba Zan Samu Amini Kamar Kwankwaso Ba - Ganduje

Gwamnan jihar Kano Dakta Abdullahi Umar Ganduje ya bayyanawa manema labarai cewa, Ba shi da kamar Kwankwaso, kamar yadda Kwankwaso ba shi da wanda ya fi Ganduje

“Zan bayar da duk lokacina domin yin sulhu da shi domin ba zan taba samun aboki kamar Kwankwaso ba iya tsawon rayuwa ta. Kuma shima ba shi da amini kamar Ganduje iya tsawon rayuwar sa".

Wannan a 2017 kenan

Tuni yan kudu sun dawo daga rakiyar Buhari, sai dakikai daga Arewa- inji Sheikh Gumi


...yace idan gaskiya ne a dora Buhari da Shagari akan mizani aga waye mai gaskiya a cikinsu

DailyNigerian ta ruwaito fitaccen Malamin Addinin Musulunci a Najeriya, Sheikh Ahmad Gumi ya soki lamirin Gwamnatin Buhari kan batun yaki da cin hanci da rashawa. Shehun Malamin yayi wannan bayani ne a wajen Tafsirin Al-Kurani da yake gabatarwa a masallacin Sultan Bello.

Ya soki lamirin hukumar yaki da cin hanci da yiwa tattalin arzikin kasa zagon kasa, musamman abinda suka yiwa tsohon Gwamnan jihar Kaduna, Alhaji Mukhtar Ramalan Yero,inda aka makala masa wani allo dauke da sunan cewar shi mai laifi ne.

Sheikh Gumi yace, “Ina kan hanya zan taho wajen Tafseer din nan ne, aka tura min wani hoto dauke da tsohon Gwamnan Kaduna Ramalan Yero yana rike da wani allo da ya nuna cewar shi mai laifi ne”

“Wannan ba daidai bane, abinda suka yi masa kuskure ne, dole ne a garemu mu gaya musu gaskiya”

“Da ya kamata Ramalan Yero ya jefar da allon yaki yadda ya daga, ba abinda zai faru in yayi haka, domin kotu ce kadai ke da ikon kama mutum da laifi”

“Batun Demokaradiyyar da ake magana, karya ake yi, domin ana take hakkin mutane”

“Idan ba dan an yafewa Shugaba Buhari laifukansa ba, da ba zai sake zama Shugaban Najeriya ba”

“Idan gaskiya ne a dora Buhari da Shagari akan mizani aga waye mai gaskiya a cikinsu”

AL'AJABI: An Haifi Yaro Dauke Da Kur'ani Da Carbi A Jihar Bauchi


...wannan raddi ne ga masu inkari da Annabi (S.A.W), cewar Sheik Dahiru Bauchi

Daga Maiwada B. Atake

Wata mata a garin Burga dake jihar Bauchi ta haifi yaro da Kur'ani da kuma carbi a hanunsa.

A yayin da matar ta zo da labarin al'ajabin zuwa gidan Shehin Malamin nan, wato Sheikh Dahiru Usman Bauchi, ta shaida cewa, wannan yaro wanda aka rada masa suna Muhammad Auwal, haka ta haife shi. Ta kuma rantse da Allah cewa wannan lamari gaskiya ne babu kokonto.

A yayain hadubar Juma'ar da ta gabata da Sheik Dahiru Bauchi ya yi, ya ce "wannan ba komai bane a wurin Ubangiji illah raddi ga kafurai masu inkari da Annabi (SAW), don kara nuna musu cewa Manzon Allah gaskiya ne.

"Sannan ya kara nuna wa duniya irin mu'ujizar Manzon Allah Sallallahu Alaihi Wasallam. Shine ya sa aka haifo wannan yaro da Kur'ani da kuma carbi".

Shehin Malamin ya kara da cewa "wannan carbi kuma ba komai bane face raddi ne ga masu inkarin Shehu Tijjani da darikarsa ta Tijjaniyya, don Allah ya kara nuna wa duniya cewa Dariku gaskiya ne.

Shehin ya kara da cewa duk ga alamomin Tijjaniyya a jikin wannan carbin. Wannan karamar Shehu Tijjani ne ta kara bayyana ga masu inkarin me Darikar ta Tijjaniyya.

A karshe Shehin ya yi addu'ar Allah ya kare Musulunci Da Musulmai, ya kuma zaunar da Nijeriya lafiya tare da kare ta daga dukkan bala'o'i.

Tuesday 29 May 2018

An Sanya Wa Katafaren Asibitin Da Sanata Shehu Sani Ya Gina Sunan Balarabe Musa

An Sanya Wa Katafaren Asibitin Da Sanata Shehu Sani Ya Gina Sunan Balarabe Musa

Da yake jawabi a yayin bikin bude Asibitin wanda ya gudana a Unguwar Bagado Kamazoo yankin Karamar Hukumar Chikum ta Jihar Kaduna, Sanata Shehu Sani ya bayyana cewar la'akari da halin kunci da kuma takura da Jama'ar yankin ke ciki dangane da batun kiwon lafiyar su, ya sanya shi zabura wajen gina musu Asibiti na zamani domin amfanin su da 'ya'yansu harma da jikoki wadanda za su zo anan gaba.

Sanatan mai wakiltar shiyyar Kaduna ta tsakiyan ya kuma kara da cewar, ya sanya wa Asibitin sunan Dattijo tsohon Gwamnan tsohuwar Jihar Kaduna Alhaji Abdulkadir Balarabe Musa, bisa ga irin kokarin da Dattijon ya ke da shi na kishi gami da taimakon talakawa inda ya bayyana shi a matsayin abin koyi ga Shugabanni na kwarai.

Da yake tofa albarkacin bakin shi dangane da muhimmin aikin da Sanatan yayi, Dattijo Balarabe Musa ya bayyana jin dadi gami da farin cikin shi akan kwazo da kokarin Sanata Shehu Sani, wanda ya bayyana shi a matsayin wakili nagari kuma Shugaba wanda ya damu da damuwar Jama'ar shi, sannan ya kara da cewar irin su Shehu Sani sune Shugabanni nagari wadanda suka dace da suja ragamar Al 'umma, wadanda ba su damu da tara abin duniya ba, babban abinda ke gaban su shine yadda za su tsamar da Jama'ar su daga halin damuwar da suke ciki.

Mista Adamu Giwa shine Sarkin Kauyen Bagado, ya mika godiyar Jama'ar shi ga Sanatan wanda suka bayyana shi a matsayin Mutum Karimi wanda baida nuna wariya ko wani bambanci a tsakanin jama'a, domin a tarihin garin nasu na Bagado babu wani Dan siyasa da ya taba kai musu dauki sai a wannan karon da Sanata Shehu Sani ya share musu hawaye, a bisa ga wannan dalilin su basu da wani Shugaban da za su zaba a yankin Kamazoo da Karamar hukumar Chikum, karamar hukuma mafi girma a jihar Kaduna mallakar Kabilar Gwari, sai Sanata Shehu Sani.

Sanatan Kaduna ta tsakiyan ya kuma jagoranci kara bude wasu manyan Asibitoci guda biyu wadanda ya gina a garin Gadagau dake yankin Karamar Hukumar Giwa, da kuma daya Asibitin dake garin Gadani ta Karamar Hukumar Igabi.
Dukkanin Al'ummomin yankin Kananan Hukumomin Uku da aka zanta da su, wato Kananan Hukumomin Giwa da Igabi da kuma Karamar hukumar Chikum, Kananan Hukumomi uku daga cikin Bakwai wanda Sanatan ke wakilta a Majalisar Dattawa, sun bayyana cewar ba su da wani Dan takara da za su zaba sai Sanata Shehu Sani a kakar zabe da ke tafe ta 2019.

Al'ummar Jihar Bauchi Sun Yi Gangamin Nuna Goyon Bayan Tazarcen Gwamna M.A A Zaben 2019

Al'ummar Jihar Bauchi Sun Yi Gangamin Nuna Goyon Bayan Tazarcen Gwamna M.A A Zaben 2019

Dandazon al'umma a jihar Bauchi wadanda suka hada maza da mata a jiya Litinin sun yi gangami zuwa fadar gwamnatin jihar domin nuna goyon bayan su ga gwamna Barista M.A Abubakar, inda suka jaddada cewa ba su da wani dan takara da ya wuce gwamnan M.A a zaben 2019.

A yayin jin ta bakin jagoran gangamin, Kabir G. Kobi Dan Hajiya, ya bayyana cewa sun yi gangamin ne domin kara jaddada goyon bayan su ga Maigirma Gwamnan Jihar Bauchi, Barista Mohammed Abdullahi Abubakar.

Da yawa daga cikin masu zanga-zangar sun bayyana cewa kasancewar sun gamsu da salon mulkin Barista M.A, babu abin da zai sanya su juya masa baya a zaben 2019.

Dalilin Da Ya Sa Zan Sake Tsayawa Takara A Zaben 2019— Ganduje

Gwamnan Kano, Abdullahi Ganduje ya tabbatar da cewa zai sake tsayawa takara a zaben 2019 don kammala ayyukan da ya fara.

Ya ce, tuni wasu mutanen kirki a jihar suka nuna masa sha'awarsu na ya sake tsayawa takara inda suka tanadar masa Naira milyan biyar don sayen fom na yin takarar.

Monday 28 May 2018

SAMA DA NERA MILYAN DARI DA RARARA YAYI SAMA DA FADI DASU ASHE FILIN KWALLO YAJE YANA GINAWA A KAUYEN KAHUTU

Daga JARIDAR DIMOKURADIYYA:

Bayan fara gudanar da bincike ana zargin kudaden da Dauda Kahutu Rarara yayi sama da fadi dasu sama da nera milyan Dari na kungiyar mawaka kauyen su Kahutu yaje yana gina filin kwallo na zamani.

Kafin lokacin Kungiyar Gwamnonin Jam'iyyar APC ta basu nera milyan 15 su bude ofishi wanda kudaden suka fada akawunt din Dauda Rarara, sai dai kawai ya kira mu yace mana ya kama ofis a (Gwamna Road) dake jihar Kaduna kuma kudaden ma duka sun kare, haka ya kama ofis din babu sanin shugaban kungiyar da matemakin sa da kuma membobin kungiya; inji Yala

Bayan an bude ofishin kungiyar, kungiyar Gwamnonin Jam'iyyar APC ta hannun Gwamnan Jihar Zamfara AbdulAziz Yari su suka bayar da kudade a matsayin tallafi, kuma Aminin Dauda Rarara Isyaku Oris ya tabbatar mun an baiwa Rarara nera milyan 100 yanzu haka suna akawunt din sa;inji Ibrahim Yala matemakin shugaban kungiyar

Da Dauda Rarara da Baban Chinedu da Isyaku Oris su suka fara tafiya maganar kudaden amma da za'a koma bai koma dasu ba.

Ibrahim Yala yace yanzu haka idan muka kira Rarara a waya baya dauka a kan maganar kudaden a saboda haka nayi shawarar saka Yanjaridu a cikin maganar 'Tunda farko nina kwana da sanin cewar Dauda ba tsakanin da Allah yake so a bude wannan kungiyar ba, yana so ne yayi amfani damu kawai'.

Saboda kin yarda daya yi azo a zauna kan kudin shi yasa aka fara zargin da kudaden yaje yana gina (Stadium) a kauyen su Kahutu dake jihar Katsina.

Har yanzu da bazata Buhari yake rawa-Tsohon Shugaban Kasa Jonathan

Tsohon Shugaban Kasa Jonathan ta bakin Mai ba shi shawara kan kafofin sadarwa na zamani a wancan lokaci Reno Omokri yace sai da Jonathan ya kirkiri fiye da ayyuka 1000 kuma ya kammala su sarai a lokacin mulkin sa wanda daga ciki akwai tsarin BVN.

A jawabin na tsohon Shugaban kasar ya hada da yi wa Adams Oshiomole raddi bayan ya zargi Gwamnatin sa da satar dukiyar Kasa.

Jonathan yace shi ya gyara filin jirgin sama na Garin Enugu ya kuma kirkiro sababbin Jami’o’i har 12.

Bayan nan Jonathan yace daga cikin ayyukan sa akwai gina Makarantun zamani na Almajirai da kuma kawo tsarin You Win da GIS domin Matasa.

Har wa yau Jonathan yace shi ya kawo wasu hanyoyin dogo da kuma tituna a Kasar.

Duk da kiran tsohon Shugaban barawo, Omokri yace gidajen da tsohon Gwamnan Edo Adams Oshiomole ya gina sun fi na Jonathan kyau, duk da cewa Jonathan din ya rike Najeriya kuma kafin nan ya rike kujerar Gwamnan Jihar Bayelsa.

Buhari Yayi Watsi Da Tsarin 'Almajiri School' Tanko Yakasai

Tsohon dan siyasa kuma uba a wannan kasa Tanko yakasai ya bayyana cewa yankin arewancin kasar nan na fuskantar kalubale tare da matsaloli ne sakamakon halin ko in kula da gwamnatin shugaba Muhammadu Buhari ke yi game da tsarin karatun Almajirai wanda tsohon shugaban kasa Goodluck Ebele Jonathan ya aiwatar.

Ko me Yasa Buhari Be Damu da Halinda Almajirai Suke Ciki ba?

NI ISIYAKU ORIS DA DAUDA RARARA MU MUKA JE MUKA KARBO NERA MILYAN 100 A HANNUN ABDULAZIZ YARI



Daga JARIDAR DIMOKURADIYYA:

Matemakin shugaban kungiyar mawaka Ibrahim Yala yace Isiyaku Oris ya tabbatar mishi da cewar Gwamnan Jihar Zamfara AbdulAziz Yari nera Milyan 100 ya baiwa Dauda Rarara ba nera milyan 60 ba.

Isiyaku Oris wanda tare suka je Wajen Gwamnan Jihar Zamfara kuma shima yana daya daga cikin mawakan kungiyar yace tabbas an baiwa Rarara kudin kungiya kuma suna hannun shi nera milyan 100.

Ibrahim Yala Wanda shine matemakin shugaban kungiyar mawaka yace yanzu idan suka kira Dauda Rarara a waya baya dauka saboda maganar kudade "kuma tun lokacin da Rarara ya bukaci mu hada wannan kungiyar na gane cewar so yake yayi amfani damu; Motocin kungiyar mu duka suna hannun shi yana ta amfani dasu.

Tunda farko shugaban kungiyar Haruna Aliyu Ningi yace Rarara yace mishi nera milyan 60 kawai aka bashi kuma daga ciki milyan sittin din ya baiwa wadanda suka yi hanya kudaden suka fito nera milyan 18, kuma ragowar nera milyan 42 da suka rage suna akawut dina kuma akawut din ya sami matsala.

To amma yanzu an tuntubi Dauda Rarara yace shi bai ma san da maganar wasu kudade ba.

Dauda Rarara a wata hira da yayi da wani Danjarida yace shi babu wanda ya bashi ne goma.

Rashin Tsaro: Abin Kunya Ne Yadda Ake Buga Misali Da Nijeriya — Jonathan


Tsohon Shugaban Kasa, Goodluck Jonathan ya bayyana  cewa abin kunya yadda a halin yanzu kasashen duniya ke buga misali da Nijeriya a matsayin kasar da Harkokin tsaro suka tabarbare.

Jonathan ya yi wannan ikirarin ne a lokacin da bude wata gada da Gwamnan Ekiti, Ayo Fayose ya gina inda ya bayar da misali da Shugaban Kasar Ghana, Nana Akufo wanda a kwanan nan ya yi izgilanci ga hukumomin Nijeriya kan rashin tabbatar da tsaro.

Gwamnan M.A Yana Iyaka Kokarinsa Wajen Aiyukan Ci Gaban Jihar Bauchi, Cewar Mataimakinsa Da Ya Yi Murabus

.... Gwamnan Bauchi ya amince da karin albashin ma'aikatan kiwon lafiya a jihar

"Kamar yadda na baiyana a cikin takardar bari na aiki, na ajiye aikina ne don bisa ra'ayina. Ina kira ga al'ummar jihar Bauchi da su rungumi gwamnatin jihar Bauchi domin cigaban jiha.

"Ban ajiye aiki na don wata manufa ba, kawai na ajiye aikina ne kasancewar na kudiri aniyar wa'adi daya zanyi akan kujerar mukaddashin gwamnan jihar Bauchi.

"Ban ajiye mukamina don tozarta gwamnati ba kamar yadda wasu ke fassara hakan, na ajiye mukamina ne kawai don kaina kuma har gobe ina tare da gwamnatin jihar Bauchi. Ina kira ga dukkan maison cigaban jihar Bauchi da ya marawa gwamnati baya domin cigaba da aiyukan alkairi wa jihar Bauchi", mamar yadda Injiniya Gidado ya bayyana.

A gefe daya kuma, Gwamnatin Bauchi karkashin jagorancin Gwamna Mohammed A. Abubakar, ta amince da biyan ma'aikatan kiwon lafiya albashin su na tsarin nan na ma'aikatan kiwon lafiya, a jihar Bauchi.

Gwamna M.A  ya amince da biyan wannan kudi kaso dari cikin dari da ma'aikatan suka jima suna neman a aiwatar musu da shi na tsarin nan na (CONMESS) da kuma na tsarin (CONHESS) na ma'aikatan kiwon lafiya na jihar bauchi

Wannan sanarwan karin data fara aiki ne a wannan wata na mayu na shekaran 2018

Mai tallafawa Gwamnan jihar Bauchi akan harkokin sadarwa Alhaji Shamsuddeen Lukman Abubakar shine ya shaidawa manema labarai hakan.

'Yan Ta'adda Sun Kashe Mutane 27 A Jihar Zamfara

Wasu 'yan bindiga sun kai hari a Zamfara inda suka kashe mutum 27 a karamar hukumar Maradun.

'Yan bindigar sun kai harin ne a ranar Juma'ar da ta gabata cikin yankin Gidan Goga da ke karamar hukumar Maradun.

Tsohon kwamishinan watsa labarai na jihar Alhaji Ibrahim Dan malikin Gidan Goga ya shaida wa BBC cewa 'yan bindigar wasu matasa ne a yankin da suka dauki bindigogi suka shiga daji.

"Sun iske manoma suna shuka da safe suka bude masu wuta bayan sun yi gargadin a kauracewa yin shuka a gonakin yankin," in ji shi.

Ya ce lamarin ya kara muni bayan da 'yan banga suka yi kokarin kai dauki, inda 'yan bindigar suka kara kashe wasu mutane baya ga manoman da suka kashe da farko.

Me ya sa babu wanda ya damu da rikicin Zamfara?Zanga-zangar matasa kan yawan kisan mutane a Zamfara

Tsohon kwamishinan ya ce yawancin mutanen kauyukan da ke yankin, bugaje ne makiyaya da ke rikici inda suke zargin juna da sace-sacen shanu, kuma yanzu rikicin ya shafi hausawa manoma.

Ya ce an tura jami'an tsaro bayan da al'amarin ya faru kuma sun janye daga yankin bayan an yi jana'izar wadanda suka mutu.

Jihar Zamfara dai na cikin jahohin arewa maso yammaci da ke fama da yawaitar kashe-kashe da sace-sacen mutane da dabbobi.

Gwamman mutane ne suka mutu a 'yan watannin da suka gabata sakamakon hare-haren da aka kai wasu kauyuka a jihar ta Zamfara.

Daruruwan mutane aka kashe a Zamfara a tsawon shekaru shida da aka kwashe ana fama da matsalar tsaro a jihar.

Sanata Kwankwaso Ya Raba Jari Ga Matasa Sama Da Dubu Uku


Daga Khadija Garba Sanusi

Sanatan Kano Ta Tsakiya, kuma tsohon gwamnan jihar Kano, Injiniya Rabi'u Musa Kwankwaso ya raba jari ga matasa 3007 dake mazabarsa.

An yi bikin raba jarin ne a yau Lahadi a dakin taro na 'THE AFFICENT' dake kan titin Magajin Rumfa a cikin garin Kano.

Koda a watanni biyu da suka gabata Sanatan ya rabawa mata zalla na mazabar tasa su 5000 jari kyauta.

Sunday 27 May 2018

Gidaje Fiye Da 100 Sun Ruguje Sakamakon Guguwa Mai Karfi A Karamar Hukumar Gumel Dake Jihar Jigawa

Gidaje Fiye Da 100 Sun Ruguje Sakamakon Guguwa Mai Karfi A Karamar Hukumar Gumel Dake Jihar Jigawa

Sakamakon Guguwa Mai Karfin Gaske Yayi Sanadiyar Rugujewar Gidaje Fiye Da Dari A Cikin Unguwar Dan Tanoma Dake  Garin Gumel  Jihar Jigawa.

Tuni Shugaban Karamar Hukumar Gumel Hon. Aminu Sani Gumel  Ya Tura Wakilci Daga Majalissar Zartawa Karamar Hukumar Gumel Domin Duba Irin Barnar Da Guguwar Tayi, Tare Da Jajantawa Al'umma Da Iftila'i Ya Samesu.

Shugaban Karamar Hukumar Yayi Matukar Jimami,Da Nuna Damuwarsa,Ganin Yadda Iskar Ta Shafi  Sama Da Gidaje Dari.

A Karshe Cikin Alhini, Karamar Hukumar Gumel Ta Jajantawa Al'ummar Da Abin Ya Shafa,Tare Da Kira a Gare Su Cewa Su Dauki  Wannan A Matsayin Wata Jarraba Daga Ubangiji.

Sannan Karamar Hukumar Gumel Karkashin Jagorancin Za6a66en Ciyaman Hon Aminu Sani  Tayi  Alkawarta,Cewa Insha Allahu Zatayi Bakin Kokarinta  Domin Mika Al'amarin Ga Hukumar Agajin Gaggawa Ta Jaha,Domin Kawo Musu Tallafin Gaggawa.

RAMADAN: Sheik Zakzaky Ya Raba Kayan Abinci Ga Mabukata

Daga Ammar Muhammad Rajab

Kamar yadda ya saba a duk shekara a lokacin azumin watan Ramadana, tun kafin gwamnati ta kama shi, Jagoran Harkar Musulunci a Nijeriya, Sheikh Ibraheem Zakzaky, yana raba kayan hatsi wadanda suka hada da Masara, Gero, Shinkafa, Suga da sauran su a irin wannan lokacin. Shekara na uku kenan (duk da yana tsare) a jere duk da Shehin Malamin gwamnatin Nijeriya na ci gaba da tsare shi, amma Shehin Malamin ya ci gaba da wannan aikin alherin ga al’umma.

A bana ma kamar kowacce shekara, an raba hatsin a inda aka saba rabawa a cikin Unguwanni na cikin karamar Hukumar Sabon gari da Zariya wanda ya hada da: Unguwannin Sabon gari, Unguwan Gwado, Hayin Ojo, Dogarawa, Tohu, Samaru, Shika, Likoro, Chikaji , Muchiya, Tudun Wada, Tudun Jukun, Zariya cikin gari, Dan Magaji, Unguwan Dankali, Wanka da sauransu.

Rabon na bana, an fara shi tun daga farkon watan Ramadanan nan har ya zuwa yau 11 ga watan Ramadan ba a kammala ba. Hakazalika a bana rabon ba a garin Zariya kadai ya isa ba, an raba a garin Kaduna. A bangaren Abuja kuwa, an raba a Mararrabar, Karmajiji, Gwarinfa, Suleja, Masaka, Gwagwalada, Lugbe da sauransu.

Idan mai karatu bai manta ba, shekaru kusan Uku ke nan, gwamnatin Nijeriya na rike da Shehin Malamin, duk da kuwa wata babbar kotun Nijeriya a karkashin mai shari’a Gabriel Kolawale ta ce a sake shi a kuma biya shi diyyar naira miliyan 50 shi da matarsa bisa tsare shi da aka yi ba da hakki ba, kuma a gina masa gida a duk inda yake so a Arewacin Nijeriya, amma har yanzu gwamnatin ba ta bi wannan umurnin ba.

Wa Zai Zama Sabon Halifan Tijjaniyya A Nijeriya?

Daga Yusuf Ibrahim Yakasai (BBC Hausa)

Tun bayan rasuwar Halifan Tijjaniya a Najeriya da kasashe makota Shaikh Isyaku Rabi'u, hankula suka fara karkata kan wanda zai gaji matsayinsa a darikar, wacce ke da dimbin mabiya.

Kawo yanzu dai mabiya darikar ta Tijjaniyya na ambata wasu shugabanni da ake ganin sun cancanci matsayin.

Sai da alama za a iya samun sabanin ra'ayi tsakanin 'yan Tijjaniyya, kasancewa kusan kowa na da nasa gwanin.

Ko da a lokacin da aka bawa Shaikh Isyaku Rabiu matsayin ma, wasu shugabannin darikar kamar Shaikh Dahiru Bauchi sun nuna rashin amincewa.

Kuma bayanai sun ce tuni ma wasu suka fara bayyana sha'awar matsayin.

Asalin halifancin Tijjaniyya a Najeriya

Halifancin darikar Tijjaniyya ya fara ne bayan shekarar 1963 lokacin da Sarkin Kano Muhammadu Sanusi na daya ya bar sarautar Kano ya koma Azare da zama.

A lokacin ne jagoran darikar ta Tijjaniyya na duniya Shaikh Ibrahim Nyass ya nada Sarki Sanusi a matsayin halifansa a Nijeriya.

Shaikh Inyas ne ya fara nada Sarki Sanusi na daya (na farko daga dama) a matsayin halifansa a shekararun 1963 bayan ya bar sarautar Kano

Shaikh Dahiru Bauchi ya shaida min cewa a shekarar ya hadu da Shaikh Nyass a birnin Makka a lokacin aikin Hajji, kuma ya ba shi sako wajen Shehunan Tijjaniyya a Najeriya musamman ma Kano da kuma Sarki Sanusi (wanda a lokacin ya koma Azare bayan barin sarautar Kano), cewa ya nada shi halifansa.

"Duk mai son ziyarata, to ya ziyarci Sanusi" In ji Shaikh Nyass, kamar yadda Shaikh Dahiru Bauchi ya fada.

Daga baya ne bayan ya dawo daga aikin Hajji, Shaikh Nyass ya aiko da takardar nada Sarki Sanusi a matysayin halifansa.

Nada Shaikh Isyaku Rabiu Khalifa

Khalifa Isyaku Rabi'u ya fuskanci kalubale bayan nada shi a matsayin Khalifan Tijjaniya a 1995.

Tun bayan rasuwar Khalifa Muhammad Sanusi a 1990, ba a nada wani a matsayin ba sai 1995 lokacin da jikokin Shehu Tijjani daga Maroko suka nada Isyaku Rabi'u a matsayin halifa.

Sai dai matakin ya haifar da takaddama tsakanin manyan darikar, inda wasu shugabanni kamar Shaikh Dahiru Bauchi suka nuna rashin amincewa da nadin.

Shikh Dahiru Bauchi ya shaida min cewa Shaikh Nyass ne kadai ke da ikon nada halifa, kuma tunda a lokacin ba ya raye, babu wanda ke da ikon nada wani a matsayin halifan Tijjaniyya.

Don haka, wasu ma na ganin Shaikh Isyaku Rabi'u sai dai ya zama halifan Sarki Sanusi, amma ba halifan Tijjaniyya ba.

To sai dai tun bayan nada Isyaku Rabiu, malamin ya rungumi al'amuran darikar ka'in da na'in, musamman wajen kashe kudi, da yi wa jikokin Shehu Tijjani da 'ya'yan Shehu Nyass hidima.

Abubuwa hudu da za a iya tuna Khalifa Isyaka Rabi'u da suYadda rayuwar marigayi Khalifa Isyaka Rabi'u ta kasance'Ba a bukatar wani halifa yanzu'

Rasuwar Shaikh Isyaku Rabi'u ta sake bude wata kofar ta neman halifancin darikar, abin da ke nuna cewa duk wanda aka nada tamkar shi ne jagoran mabiya darikar a Najeriya.

Wasu jagororin darikar na ganin babu bukatar nada wani halifa, tunda batun halifancin ba ya cikin sharuda ko ka'idoji na darikar ta Tijjaniyya.

Babban limamin masallacin Abuja Shikh Ibrahim Ahmad Maqri na ganin batun halifanci a darikar ta Tijjaniyya ba wani abu ne mai muhimmanci ba, abin da ya ke mafi muhimmaci shi ne kiyaye ka'idojin darikar da yin aiki da su, da kuma hada kan jama'a.

Shaikh Maqri ya ce ko da nadin da aka yi wa Sarkin Kano Sanusi I "dalili ne na addini, dalili ne zumunci, dalili ne na karfafar 'yan uwantaka, da kuma rage damuwa na abin da ya faru da Khalifa Sanusi".

To amma ganin yadda zamani yake sauyawa da kuma yadda aka shafe shekaru sama da 20 'yan darikar ta Tijjaniyya suna daukar Shaikh Isyaku Rabi'u a matsayin jagora zai yi wuya yanzu su zauna ba tare da jagora ba.

Wa zai karbi mukamin a yanzu?

Tuni dai wasu a darikar suka fara yunkurin neman wanda zai zama sabon Khalifa, kuma da alama za a iya kai ruwa-rana.

Shaikh Dahiru Bauchi.

Shaikh Dahiru Bauchi ya ce ya wuce a ce za a nada shi halifancin Tijjaniyya a yanzu, domin tuni Shehu Inyass ya nada suYana daga cikin almajiran Shaikh Ibrahim Inyass 'yan kadan da suka rage a rayeTun a zamanin Shikh Inyass yana cikin mutanen da ke kare darikar Tijjaniyya da yadataShaikh Inyass da kansa ya ambace shi "Kakakin Faida (Lisanul Faidati)"Mahaddacin Al-kur'ani ne kuma yana daga cikin manyan malamai a NajeriyaWasu na ganin shekarunsa sun ja don haka bai kamata a kara masa wani nauyi ba

To amma a tattaunawar da muka yi da shi Shaikh Dahiru Bauchi ya ce shi ba ma ya bukatar matsayin, domin kuwa tuni Saikh Inyass ya nada shi halifansa tare da wasu manyan darikar.

"Ai ni na wuce nan, Shaikh Ibrahim da kansa ne ya nada mu halifofi mu, kuma shi kadai yake da iko ya dauki daya daga cikinmu ya daura a kan mu gaba daya," in ji malamin.

Ya kara da cewa, "Shi halifa a cikin Tijjaniyya kamar janar ne a cikin soja, ba guda daya ba ne, don haka kowa ya san wanda ya fi shi."

Wasu jagorori a darikar Tijjaniyya na ganin Shaikh Dahiru Bauchi ba ya ma bukatar wani nadi na musamman, duba da irin matsayinsa a darikar da yadda yake da mabiya, da kuma iliminsa.

Sarkin Kano Muhammad Sanusi II

Sarkin Kano Muhammadu Sanusi na daga wandada ake ganin sun cancanci matsayin halifancin tijjaniya a Najeriya, matsayin da asali kakansa ne ya fara rikewa.

Asalin mukamin dai na Sarkin Kano Sanusi na daya ne, wato kakan sarki na yanzu. Sarkin Kano na yanzu ya kama harkar darikar sosai bayan ya zama sarki. Ya taba bayyana cewa gwaninsa shi ne Sarkin Sanusi na daya, kuma yana so ya gaje shi. Yanzu yana da mulki da kudin da zai iya yi wa darikar hidima fiye da wasu shugabannin da damaYana da ilimin addini da na zamani, kuma yana kara samun karbuwa a tsakanin wasu musulmin NajeriyaYa ci gaba da jagorantar zikirin Juma'a da ake yi duk shekara a gidan Sarkin Kano, wanda aka fara a zamanin Marigayi Ado Bayero.

Wasu bayanai na nuna cewa tuni wasu mabiya darikar da kuma wasu makusantan sarkin suka fara nuna cancantarsa.

Shaikh Shariff Ibrahim Saleh

Wani babban jagoran da ake ganin ya kamata ya zama jagoran mabiya darikar ta Tijjaniyya a Najeriya shi ne Shaikh Shariff Ibrahim Saleh Alhusayniy.

Yana daga cikin manyan malam darikar Tijjaniyya da Musulunci baki dayaYa yi karatu a wajen manyan malamai sama da 300 a kusan dukkan kasashen musulmai na duniyaYa yi karatu a wajen Shaikh Inyass, kuma wasu na yi masa kallon daya daga manyan almajiransaWasu na ganin ya fi kowa cancantar zama jagoran darikar a Nijeriya

To amma malamin bai fiya shiga cikin al'amuran shugabanci ba, ya fi maida hankali wajen karantarwa da rubuce-rubuce da bada fatawa da kuma tafiye-tafiye.

Don haka wasu na ganin ko da an yi masa tayi da wuya ya karba.

Da gaske ne Shehu Ibrahim Nyass ya bayyana a Maulidin Abuja?Ganin Shehu Ibrahim Nyass karama ce - Dahiru BauchiAikin da ke gaban sabon jagoran Tijjaniyya a Najeriya

Nijeriya ita ce kasar da ta fi yawan jama'a a nahiyar Afirka, kuma yawan mabiya darikar a kasar ya zarta na kowacce kasa a nahiyar.

Kuma saboda muhimmancin da Shehu Inyass ya nuna na kasar a fuskar darika, ya sa wasu ke kallonta a matsayin cibiyar darikar bayan Maroko da Senagal.

Don haka duk wanda zai zama jagora tamakar ya dauki nauyin 'yan darikar ne a kasar da wasu kasashe makwabta kamar Nijar da Ghana da sauransu.

Shaikh Maqari na ganin babban abinda ya kamata ya sa a gaba kamar hada kan 'yan darikar da sauran musulmin kasar, musamman wadanda suke da sabanin fahimta.

Yace kuma dole ne sabon jagoran darikar ya maida hankali wajen nisanta darikar da bara-guri da suke aikata wasu abubuwa da suka ci karo da addinin musulunci, kuma suka fakewa da sunan darikar.

Wasu malaman darikar kuma na ganin dole ne a yi cikakken nazari kafin a zabo wanda zai zama jagoran darikar.

Malamai kamar Shaikh Nura Muhammad Arzai na cewa dole a samu mai jajircewa, tsayayye, mai kamewa mai tsayawa a kan manufa.

Ya ce ana bukatar mai cikakken ilimi na addini da na zamani.

Malamin ya kara da cewa ana bukatar sabon jagoran ya zama yana da wadata da zai iya kamewa daga abin hannun mutane, kuma zai iya daukar nauyin gudanar da al'amuran darikar.

A yanzu dai za a zuba ido a ga yadda za ta kaya musamman ganin irin tasiri da mukamin ke da shi a darikar ta Tijjaniya.

Darikar Tijjaniya a takaice

An kafa darikar ne a kasar Aljeriya a shekarar 1784. Sheikh Ahmad ibn Muhammad al-Tijjani ne ya kafa ta. Ta yadu zuwa sassan duniya daban-daban, inda ta ke da mafi yawan mabiyanta a Arewaci da kuma Yammacin AfirkaTana kuma da karin mabiya a Afirka Ta Kudu, da Indunisiya da kuma sauran sassan duniya. Akwai sauran dariku na Sufaye a addininin Musulunci amma Tijjaniya ta fi kowacce girmaSun ce suna da muhimman ayyukan ibada guda uku a kowace rana:Neman gafarar Allah; Yin salati ga Annabi Muhammad (SAW) da kuma kadaita AllahSai dai ana zarginsu da wuce gona da iri wurin nuna soyayya ga Shehunnansu, lamarin da wasun su ke musanta waAna alakanta Sheikh Ibrahim Nyass da farfado da darikar a karni na 20 bayan ta kwanta damaAn haife shi a kasar Senegal kuma jama'a kan yi tattaki daga sassan nahiyar da dama domin ziyartar kabarinsaDarikar Tijjaniya ta kasu kashi-kashi musamman a kasashe irin su Nijeriya inda suke da mabiya sosai.

Shehu Sani da Hunkuyi suna gab da ficewa daga jam'iyyar APC, dalilansu...

Wani bangare na jam'iyyar APC da ke karkashin jagorancin Sanata Suleiman Hunkuyi da ke wakiltar Kaduna ta arewa da Sanata Shehu Sani mai wakiltar Kaduna ta tsakiya sun ce akwai yiwuwar za su fice daga jam'iyyar.

A wata sanarwa da suka fitar a jiya Juma'a, sanatocin biyu da ke kiran kansu da suna APC Akida sunce sun kammala bita akan jam'iyyar da matsalolin shugabancin da ke adabar jam'iyyar a jiha da ma kasa kuma suna tunanin ficewa daga jam'iyyar da suka taimaka wajan kafawa.

APC Akida ta ce za ta dauki matakin ficewa ne "Idan babu wata kwakwarar alamar samun nasara wajen magance matsalolin wariyar da kuntatawa da ake yiwa wasu yan jam'iyyar a jihar Kaduna"

Shugaban kungiyar, Tom Maiyashi, wanda ya fitar da sanarwar ya ce akwai wasu abubuwa guda biyu da suka faru a jihar wanda suka tabbatar masa da cewa babu shugabanci na gari a jam'iyyar APC reshen jihar Kaduna kamar yadda The Cable ta rawaito.

"Yadda aka gudanar da zabukan shugabanin jam'iyya da kuma zabukan kananan hukumomi a jihar ya tabbatar min da cewa rashin jagoranci mai kyau zai dushe duk wani farin jini da jam'iyyar ke dashi a jihar."

Dama dai kungiyar APC Akida ta bayyana yiwuwar faruwar hakan tun da fari lokacin da ta lura da irin kamun ludayin gwamna Nasir El-Rufai," a cewar Maiyashi.

A saboda wannan dalilan ne kungiyar ke kira ga duk wadanda gwamna El-Rufai ke ganin girmansu da su hanzarta jan kunnensa domin kare jam'iyyar daga fadawa cikin bala'i.

Kungiyar kuma ta sanar da mahukuntan jam'iyyar a jiha da kasa cewa za su fice daga jam'iyyar idan har ba'a yi gyara ba.

Matasa biyu sun mutu wajan murnar sakin Jonah Jang

Bayan da kotu ta bayar da belin tsohon gwamna  jihar Flato, Jonah Jang,
magoya bayansa da dama ne suka tare shi suna nuna murnarsu da wannan saki da aka mishi,

matasa daga yankin Tudun Wada na jihar sun rika wasa da mota akan tituna dan nuna murna inda aka samu tsautsayi har biyu daga ciki suka mutu.

Sirfwang Kefas da Jerry Sunday na daga cikin wadanda ke nuna irin wannan murna yayin da suke cikin mota ana tukin ganganci dasu, motar ta kwacewa direban inda ta kauce hanya dalilin haka matasan biyu suka rasa rayukansu, kamar yanda jaridar Daily Trust ta rawaito.

Matasa da dama ne suka fito suna nuna goyon baya ga Sanatan wanda ake tuhumarshi bisa barnatar da kudi sama da biliyan shida.

Rarara Ya Awon Gaba Da Kudin Kungiyar Mawaka Har Naira Milyan Dari


JARIDAR DIMOKURADIYYA

Anyi cirko-cirko a Ofishin kungiyar mawaka tun bayan bullar rahoton mawaki Dauda Kahutu Rarara yayi kwana da makuden kudade sama da nera milyan Dari.

Shugaban kungiyar mawakan na yankin Arewa Haruna Aliyu Ningi dake jihar Bauchi shiya bayyanawa manema labaru, yace Gwamnan Jihar Zamfara shiya basu kudin bayan sun bukacin hakan kan irin gudun mawar da suka bayar a gabanin zabukan 2015 gashi kuma sun shirya bayar da gagarumar gudun mawa a zabukan 2019 dake tafe.

Tunda farko Dauda Rarara shiya shige gaba wajen karbo kudaden kuma ya tabbatar mun da cewar Gwamnan Jihar Zamfara AbdulAziz Yari ya fara basu nera Milyan Sittin sai dai wadanda suka yi hanya har aka bayar da kudaden ya basu nera milyan goma sha takwas inji Haruna Ningi.

Ya kara da cewar a matsayina na shugaban kungiya har zuwa yau Dauda bai taba yi mun maganar ba, bayan lokacin dana sake tun tuba sa sai yace har yanzu ba'a cika ragowar kudaden ba amma na kusa dashi wanda shima yana daga cikin mawakan mai suna Oris yace tuni an baiwa Rarara ragowar nera milyan Arba'in din.

To a hakan dai muka bukaci nera milyan Arba'in da biyu da suka rage a hannun shi ya kawo su azo a zauna a tattauna a kan su sai yace wai asusun ajiyar shi na banki ya sami matsala.

Buhari Ya Soke Kwangilar Makaman Isra’ila Ta Dala Miliyan 195

Shugaba Muhammadu Buhari ya soke kwangilar nan ta sake sayo kayan tsaro, wadda ministocin sa suka kirkiro, saboda zargin harkalla a cikin kwangilar.

Kwangilar wadda Ministocin suka sa wa hannun a cikin watan Disamba, 2017, an rattaba cewa za a bai wa kamfanin kwangilar mai suna HSLi zungurutun kudi har dala milyan 195, shi kuma zai kawo jiragen yaki da helikwafta da kuma jirage kanana na yaki na ruwa, 12 daga Isra’ila.

An ce Ministan Harkokin Sufuri, Rotimi Amaechi ne ya shirya kwangilar, yayin da masu sukar lamarin suka ce an kirkiri kwangilar ne domin a saci kudade kawai.

Shugaban Ma’aikatan Fadar Shugaban Kasa, Abba Kyari ne ya rubuta wa Antoni Janar na Najeriya, Abubakar Malami wasika cewa a soke kwangilar.

Sannan kuma Buhari ya umarci mai ba shi shawara kan harkokin tsaro da kuma hukumar liken asiri ta kasa da su binciki yadda kamfanin ya samu yarjewar yin kwangilar ba tare da samun satifiket na gangariyar amincewa da tabbacin ko sahihancin yay i kwangila a kasar Isra’ila ba.

Sannan kuma Buhari ya bada umarnin cewa kamfanin kwangilar ya kawo kayayyaki na dala miliyan 50, wato na adadin kudin da aka fara ba shi a matsayin somin-tabi tun kafin ya fara kawo komai.

Binciken da Arewa Dailypost ta gudanar ya nuna cewa kamfanin HSLi ba shi ma da rajista a kasar Isra’ila, amma sai ya hada baki da wani kamfani na kasar Isra’la mai suna Mitrelli, wanda aka ce kamfanin ya na da alaka ta kusanci da Minista Ameachi.

Cikin 2012 a lokacin da Ameachi ke gwamnan jihar Rivers, ya taba bai wa Mitrelli kwangilar aikin wata gona a can gefen Fatakwal har ta tsabar kudi dala milyan 140.

A da can babu ruwan Mitrelli da harkar makamai, amma a dare daya kamfanin ya tsoma kan sa a cikin kwangilar makamai.

An gurfanar da dan Atiku a gaban kotu saboda ya gaza biyan alawus din 'ya'yan sa

A ranar Larabar data gabata ne wata babbar kotu da ke zamanta a Igbosere jihar Legas ta saurari karar da aka shigar a kan, Aminu Atiku, dan tsohon mataimakin shugaban kasa Atiku Abubakar saboda rashin biyan kudin kulawa da yaransa N250,000 duk wata da bai biya ba tun watan Fabrairun 2018.

Sai dai Aminu Atiku ya shaidawa Alkali kazeem Alogba cewa yana daukan dawainiyar duk bukatu na yaransa.

Mai shari'a Alogba zai zartas da hukunci a kan wata bukata da Atiku ya shigar a kotun inda ya ke rokon a janye kudin wata na kulawa da yaran da kotu ta gindaya masa a baya.

Kotun ta tsayar da cewa a rannan ne zata zartas da hukuncin bayan jin muhawarrar da lauyan Atiku, Oyinkan Badejo da kuma Ethel Okoh, lauyan tsohuwar matarsa,Ms Ummi Fatima Bolori suka tafka.

Atiku da tsohuwar matarsa Bolori duk basu samu halartar kotun ba.

A karar da ya shigar,Aminu Atiku yana rokon kotun ta canja hukuncin da wata kotun ta zartar a baya inda aka dankawa tsohuwar matar rainon yaransu Ameera mai shekaru 11 da kuma Aamir mai shekaru 7.

Da aka fara sauraron karar a ranar Larabar, Badejo ta bayyana cewa akwai alamar tambaya a kan biyan N250,000 a kowanne wata da aka dorawa Aminu Atikun duk da cewa yana daukan nauyin dawainiyar yaran.

A cewarta,Aminu Atikun yana dauke dukkan nauyin yaransa wanda suka hada da biyan kudin makarantarsu tare da kudin magani da sauransu.

Lauyan ta ce kotun da ta yanke wannan hukuncin ba ta yi la'akari da karfin aljihun Atikun ba shi yasa ta dora masa N250,000 a duk wata, ta kara da cewa bai dace ayi la'akari da dukiyar da iyayen Aminu Atikun suka mallaka ba.

Sai Lauyan Bolori, Okoh ta kallubalanci wannan zancen.
Ta ce tun da Atikun bai biya kudin kulawa da yaran ba tun watan Maris, inda ta kara da cewa rashin biyan kudin kulawa da yaran ya sabawa sashi na 62(5) na dokar kiyaye hakkin yara.

Ta yi ikirarin cewa Atiku bai biya kudin makarantar yaransa ba sai ranar 11 ga watan Afrilu, kwana daya kafin kotun ta saurari karar.