Friday 20 April 2018

An Fatattaki Wuraren Sayar Da Barasa Da Gidajen Karuwai A Jigawa

Biyo Bayan Zaman Kwamitin Kula Da Harkokin Tsaro Na Karamar Hukumar Hadejia Da Kuma Zaman Majalisar kansiloli Na Karamar Hukumar Da Aka Gudanar A Jiya Alhamis, Kwamitin Tsaro Na Karamar Hukuma Ya Karbi Koke-Koken Al'ummar Daban-daban Musamman Mutanen Dake Zaune A Unguwar Mai Randa Dake Kan Hanyar Kano Cikin Garin Hadejia, Dangane Da Yadda Wasu Tsiraru Suka Mayar Da Yankunan Matattarar Gidajen Siyar Da Barasa Da Bude Gidajen Mata Masu Zaman Kansu.

Sakamakon Karbar wannan Koke Da Yadda Hakan Ke Yin Barazana Da Zaman Lafiyar Al'umma Hadi Da Yinn Karan Tsaye Da  Addini Da Al'adun  Karamar Hukumar Hadejia.

Majalissar Kansilolin Karamar Hukumar  Bisa Jagorancin Kakakin Majalisaar Hon Dawaki Baffa, Hade Da Majalissar Harkokin Tsaro Na Karamar Hukumar Sun Zartar  Da Dokar Hana Sayar Da Giya A Dukkan Fadin Karamar Hukumar  Tareda Gidajen Mata Masu Zaman Kansu.

Inda A Yau Majalissar Kula Da Harkokin Tsaro Na Karamar Hukumar  Hadejia Wadda Ya Kunshi Shugaban Karamar Hukumar, Da Mataimakinsa,  Rundunonin Tsaro Na Yan sanda, DSS, Hisbah, Civil Defence, Immigration, Prison Service, Jamian Sojoji, Vigilante Dasauransu.

Sannan Kuma da Dukkannin Majalissar kansilolin Karamar Hukumar, Sukayi Tataki Zuwa Wannan Gidaje Dake Unguwar Mai Randa, Wajen Kulle Dukkannin Wannan Gidaje Na Sayar Da Giya Da Aiyukan Badala.

No comments:

Post a Comment