Thursday 24 May 2018

A lokacin da nake mulkin Soji bana jin shakkar kowa – Shugaba Buhari

A jiya ne Shugaban kasa Muhammadu Buhari ya gana da ‘Yan kungiyar BSO ta Magoya bayan sa a fadar Shugaban kasar da ke Aso Villa inda ya tattauna da su kan batutuwan da su ka shafi halin kasar.

Buhari yace IBB ya saki barayin da ya daure kuma aka zauna lafiya

Shugaban kasa Muhammadu Buhari ya bayyana cewa Gwamnatin sa na matukar kokari duk da halin da ta tsinci kan Kasar nan.

Shugaban Kasa Buhari yake cewa babu Shugaban kasar da ya kashe kudi wajen gina titi da hanyoyi irin sa.

Shugaba Buhari yace Gwamnatin nan ta kashe sama da Tiriliyan 1.3 cikin bara da bana kurum domin gina hanyoyi da sauran abubuwan more rayuwa a Najeriya.
Inda Kafin nan dai an bar tituna da hanyoyin dogo sun lalace kwarai a Kasar.

Bayan haka Shugaban kasar yace a lokacin da yake mulkin Soji sai da ya kama duk Shugabannin kasar ya daure saboda zargin sata illa wanda ya iya karbar kan sa.

Sai dai yace a wannan tsarin Damukaradiyya sam hakan ba zai yiwu ba.

Shugaba Buhari yace da yake mulkin Soja tsakanin 1983 zuwa1985 har Shugaban kasa sai da ya daure.
Sai dai kuma bayan an kifar da Gwamnatin sa, sai da aka daure shi kansa sannan kuma aka maidawa barayin kasar duk kudaden da suka sata.

No comments:

Post a Comment