Sunday 13 May 2018

AMBALIYAR RUWA A KANO: Gyara Kayanka Dai Ba Zai Zama Sauke Mu Raba Ba

DAGA ABBA ADAM ISAH

A madadin 'yan karamar hukumar Fagge matsabar Kwachiri muna kira da babbar murya akan a taimaka a fitar da mu wannan kangi da muke cikin na wannan aiki na alkairi da Dan majalisar jiha na kano da ya fara, amma yana nema ya zama aika-aika ga mazauna yankin. Saboda yadda ruwa ya yi ambaliya har cikin dakunan mutane, katifu da gadaje suna yawo saman ruwa. Hakan zai sa mazauna yankin su kasance cikin fargaba a duk lokacin da hadari ya hadu za a yi ruwa kai koda iska mai karfi ce ta kada sai hankulansu sun tashi saboda hali na ni 'ya su da suke tunanin za su shiga idan ruwan sama ya sauka.

Ya kamata dai idan dama an tsiri yin wannan aiki ne ya zama kwalli na kanfen 2019 to ga wata shawara a bi gidaje daya bayan daya a raba musu kwale-kwale domin tsallake ruwa idan gari ya waye domin siyo abun kari da kuma kai yara makaranta da fita harkokin yau da kullum saboda matasan yankunan ko zama da dogon wando ba sa yi saboda gudun kota kwanan ceton tsofaffi da kuma tsallakar da yara kanana daga gaba zuwa gaba.

No comments:

Post a Comment