Thursday 24 May 2018

An bukaci Shugaba Buhari ya cunawa Obasanjo da Jonathan hukumar EFCC

Wata kungiya mai zaman kanta a Najeriya dake rajin kare martabar dan adam da kuma tabbatuwar demokradiyya watau Socio-Economic Rights and Accountability Project (SERAP) a turance ta bukaci gwamnatin tarayya da ta soma binciken tsaffin shugabannin kasar Najeriya game da yadda suka tafiyar da harkar wutar lantarkin kasar.

SERAP a cikin wata sanarwa da ta fitar ta rabawa manema labarai, ta bayyana cewa abun takaici ne a kashe kusan dalar Amurka biliyan 16 a harkar wutar lantarkin amma har yanzu ba ta canza zane ba.

Daga nan sai kungiyar ta shawarci shugaban kasar da ya mika tsaffin shugabannin kasar ga hukumomin binciken da suka kamata domin gudanar da bincike a kan su.

No comments:

Post a Comment