Wednesday 16 May 2018

Anga watan Ramadan a Zamafara da wasu jihohi

Rahotanni daga jahar Zamfara da kuma wasu sassan Nigeria suna bayyana cewa anga jaririn watan Ramadan.

Hausa Times ta ruwaito tuni masallatai a Jihar Kaduna da wasu sassan kasarnan suka fara sanarwa a lasifika domin jama'a su dauki harama. Kazalika Hausa Times ta ruwaito tuni wasu masallatan suka fara gudanar da sallar tarawihi a yau.

Kawo yanzu dai ana dakon sanarwa a hukumance daga fadar mai alfarma Sarkin Musulmi wanda shi keda hurumin bayar da sanarwa.

No comments:

Post a Comment