Thursday 24 May 2018

EFCC Ta Sake Kama Shekarau


▪ Gobe Za A Gurfanar Da Shi Gaban Kotu

Rahotanni daga Kano sun tabbatar da cewa a halin yanzu Tsohon Gwamnan Kano, Ibrahim Shekarau yana tsare a ofishin hukumar EFCC da ke jihar Kano.

Daruruwan magoya bayan Shekarau ne dai suka yi cincirindo a titin Dandalin mahajjata inda suka yi kokarin hana tsohon gwamnan shiga ofishin EFCC wanda ya isa wurin da misalin Karfe hudu na Yamma, lamarin da ya janyo aka karo jami'an tsaro wadanda suka yi amfani da borkonon tsohuwa wajen tarwatsa magoya bayan Shekarau.

A gobe Alhamis ne dai, hukuma za ta gurfanar da tsohon Gwamnan a gaban kotun tarayya da ke Kano shi da Aminu Wali da Mansur Ahmed bisa laifin karbar Naira Milyan 950 daga hannun Tsohuwar Ministar Mai, Alison Deizani Madueke a lokacin zaben 2015. Sai dai Kakakin Tsohon Gwamnan, Sule Sule ya nuna cewa an tuhumi Shekarau ne saboda ya caccaki gwamnatin Shugaba Buhari.

No comments:

Post a Comment