Saturday 12 May 2018

Kotu Ta Tabbatar Da Gwamna M.A Abubakar A Matsayin Halastaccen Gwamnan Bauchi

Kotun koli ta tabbatar da Barista Muhammad Abdullahi Abubakar a matsayin halataccen Gwamnan jihar Bauchi.

Idan ba a manta ba, Abdullahi Tanko Orlando ya gabatar da kara a gaban Kotu har ta kai ga Kotun koli na kalubalantar zaben fidda gwani da jam'iyyar APC ta yi a lokacin zaben fitar da gwani a 2015 wanda M.A ya yi nasara.

A yayin yanke hukunci a yau Juma'a Alkalin Kotun babban mai Shara'a, Mai Shari'a Utterle ya ce Tanko a karkashin doka ba shi da hurumin kalubalantar zaben fitar da gwani bayan an yi babban zabe.

Majiyar da cewa Shari'ar mai lamba ST/854/2015 ta kawo karshe a yau tare da tabbatar da Batista Mohammed Abdullahi Abubakar a matsayin Gwamna mai cikakken iko.

No comments:

Post a Comment