Friday 18 May 2018

Najeriya zata hadu da fushin Allah idan gwamnati bata saki El-Zakzaky ba – Sheikh Dahiru Bauchi

Babban malamin nan a Najeriya Sheikh dahiru usman Bauchi yayi kira ga gwamnatin shugaban kasa Muhammadu Buhari da a zauna domin tattaunawa game da Shugaban kungiyar shi’a El-zakzaky.

A cewarsa ya kamata a samu mafita domin a sake shi ya je ya nemi lafiya, idan har gwamnati tayi haka to lallai babu shakka za'a kara samun zaman lafiya a kasar.

Shehin malamin yaci gaba da cewa kin sakin El-zakzaky wata jarabawa ce da Allah zai jarabci wannan kasar da ita, saboda shugaban shi’an malamine na addinin musulunci, sannan kuma  tsare shi ba tare da wata hujja ba ,kuma ba'a nuna alamar yana da laifi ba ,to lallai Allah zaiyi fushi da wannan kasar.

Sheik Dahiru Bauchi ya kammala bayanansa da cewar malamai dai sune magada annabawa idan aka muzguna masu to babu shakka za'a fuskanci fushin Allah, kuma shi fushin Allah babu dan ba ruwa na kowa da kowa zata shafa.

Daga karshe shehin ya bawa gwamnati shawara data saki El-zakzaky a nema masa lafiya a kasar waje.

No comments:

Post a Comment