Wednesday 16 May 2018

NAYI NADAMAR AURE NA FARKO~ Fati Muhammad


Daga Nijeriyarmu a yau

Tsohuwar fitacciyar jarumar nan ta masana’antar Kannywood, Fati Muhammad, ta bayyana auren jarumi Sani Musa Mai Iska a matsayin babbar nadamar ta a rayuwa.

Jarumar ta bayyana hakan ne a cikin wata hira da tayi da Manema labaru inda ta bayyana cewa ta amince da cewa kowa na da jarrabawar da Allah ya ke yi masa sannan kuma tace ita dai jarabawarta ta fannin aure take.

Jarumar ta kara nanata maganarta da tayi a baya inda tace ba fa zata kara auren dan fim ba koma waye.

Daga karshe kuma jarumar ta bayyana jarumi Ali Nuhu a matsayin wanda take darajtawa fiye da kowa a masana’antar fim; kamar yadda majiyar Al'ummata ta wallafa


Idan za ku iya tunawa Fati Muhammad ita ce ta fito a cikin tsohon fim din nan na Sangaya tare da jarumi Ali Nuhu, a matsayin Zubain,
Babu shakka annan fim din ne ya fito da ita.

No comments:

Post a Comment