Friday 18 May 2018

Shugaba Buhari ya saki kudi domin yashe kogin Kwara don arewa ta karbi jiragen ruwa.

Zaman majalisar kasa na wannan mako, ya sahale sakin biliyoyin nairori, wadanda za'a yi amfani dasu don jawo teku zuwa arewacin kasar nan har zuwa jigar Neja, dama sayo wasu jiragen ruwa da kudin Turai Yuro 21m don jawo jiragen maqare da kaya zuwa arewa.

Ministan Sufuri shine ya bada wadannan bayanai a jiya laraba, bayan zaman na majalisar kasar,
inda ya fayyace yadda za'a fara aikin, wanda a baya shugaba Umaru Musa Yar aduwa ya saki kudi don ayi, amma daga rasuwar sa, wanda ya gaje shi, ya dakile aikin.

Anyi hakan ne don saukaka cunkoso a gabar tekun ta kudu, da saukaka wa arewa shigo da kaya har yankin cikin sauki, inda za'a fara sauke kaya a Baro ta jihar Neja.

Za dai a fadada wasu yankuna na ruwan na Neja, wanda aka baiwa wani kamfani Biara Concept Nig. Ltd.

A gefe guda kuma, za'a samar da gada a garin Karu, sai aikin ruwa a jihar Bauci da Calabar, da wasu manyan tituna da zasu hado kudu da arewar kasar nan.

Yawanci ayyukan shekaru biyu zasu dauka ana yi duk da dai Saura shekara daya wannan zango na mulki ya kare, shuwagabannin su mika mulki ga wasu zababbu, ko kuma su zarce a karo na biyu in an zabo su.

No comments:

Post a Comment